Bakar Inuwa Hausa Novel Hausa Novels

Bakar Inuwa 17


Bakar Inuwa 17
Viral

Episode 17_*

…………★Raudha na zaune yau an cire ƙafar tata a jikin ƙarfen dan kumburin ya sauka sosai, maimakon tayi ramar ciwo sai ta ƙara haske da ƙyau saboda samun canjin waje, ga abinci mai ƙyau ga a.c.
Idanu taɗan waro saboda mamakin ganin mahaifin nasu, cikin rawan baki tace, “Abbanmu!”.
Wannan kawai ta isa amsa ga bappi, dan cike da zumuɗi shima M. Dauda ya nufa gadon yana ware hannuwa wai zai ringume Raudha irin na turawa kar Bappi ya rainasu yaga su ƴan ƙauyene basu iya tattalin ƴaƴa ba. Sai dai kuma tunkan ya ƙaraso Raudha tai saurin ɗaukar filo ta tareshi tana faɗin, “Abbanmu lafiya?”.
Sosai dariya ta nema kufcema Bappi, yay ƙoƙarin kauda kansa yanayi ƙasa-ƙasa. Dan M. Gambo ya matsa da sauri ya ɗirkama M. Dauda dundu a baya. “M. Dauda ka nutsu mana miye haka zaka zubar mana da mutunci”.
Harararsa M. Dauda yayi, cikin yin ƙasa da murya yace, “Kai baka gane ba, idan ba’ayi hakan ba ai sai attajirin nan ya ɗauka bama kula da ƴaƴanmu, kasan su haka sukema ƴaƴansu kamar larabawa da turawa. Ko so kake yay tunanin dan munga sun raɓesune muka fara son su”.
“Eh kumafa hakane kayi gaskiya, sai dai kasan Raudhatu ustaziya ce bazata yarda ba fa, karma kaja ta bamu kunyar datafi wadda muke gudu”.
Duk zancen nasu sarai Bappi najinsu duk da a hankali sukeyi, dan shi ALLAH ya bashi ƙarfin ji, zama a iya cewa a wajensa Ramadhan ya gado ƙarfin ji, ko yaya kai magana kusa da su sai sunjika da izinin ALLAH, dan haka yay saurin katsesu dan karsu kasheshi da dariya. Ya gyara tsaiwarsa dayin gyaran murya yana faɗin, “Ya kamata ku dubata sai muje muyi sallar magrib, na kuma san masaukinku……”
Kafinma ya kai ƙarshe M Gambo ya katsesa da faɗin, “Ai bamu da wani masauki yallaɓai, dan shi M. Dauda ya rabu da gyatumar tata shiyyasa ta taho nan ita da yaran wajen tata gyatumar. Dama yanzu haka munzo biko ne da duba jikin Raudhatun”.
Raudha dake jin tamkar ta fasa ihu dan takaicinsu ta kauda kanta gefe idanunta na tara ƙwalla. Tana son mahaifinta, tana kuma fatan ya nutsu ya bar duk abinda yakeyi na ashsha, sannan sam bata baƙin cikin nunasa matsayin uba dan bata da kamarsa..
Bappi yay saurin dakatar dasu, “Ok ok babu damuwa muje muyi sallan first dai yanzu, sai musan abunyi kamar zaifi”.
Badan sun so ba suka bisa. Dan gaba ɗayansu idonsu nakan Haɗaɗɗun kulolin abincin dake gefen gadon Raudhan. Sai haɗiyar yawu suke tunkan suga abinda ke a ciki.

Suna fita doctor na shigowa. Hakan yasa Raudha roƙonsa aron waya dan gara ta kira Mommy ita kam bazata iya da halin Abba ba. Shima Dr Shamsu ya gamsu da hakan, dan haka babu musu ya bata ta saka number Mommyn, cikin sa’a kuwa bugu ɗaya aka ɗaga. Wani daɗi ya kama Asabe saboda jin muryar Raudhan Alhmdllhi, duk da dai da safe sunzo asibitin dubata ita da Aunty Hannah ma.
“Mommy dan ALLAH kizo asibiti wlhy Abba ne yazo shida baba Gambo”
Zumbur Asabe ta miƙe har tana neman yadda zani. Shi dauda ɗinne yazo Bingo harma asibitin da kike?”.
“Wlhy kuwa mommy gasu ma tare da baba alhaji (Bappi take kira haka). Yanzu ya jasu suka tafi massallaci”.
“Innalillahi wa-inna’ilaihirraji’un. Ashe kuwa zanci kaza kazan ubansu a garin nan. Ni yanzu babbar matsalata baza’a barni shiga asibitin ba….”
“Mommy dan ALLAH ki kwantar da hankalinki banga abin faɗa anan ba. Kizo asibitin Doctor zai shigo dake yace. Amma mommy dan ALLAH karki tayasa kuyi rikici Please”.
Tai maganar tamkar zatai kuka. “To” kawai asaben tace mata ta yanke wayar, badan tasan zata iya bin maganar Raudha ɗin ba.

*_BINA STATE PLACE_*

“Ranka ya daɗe bakace komai ba”.
Fulani ta faɗa a hankali cike da ƙasaita tana duban mai-martaba dake kishingiɗe a tsakkiyar falon hutawarsa da ko iyalan nasa ba kowacce keda ikon shigarsaba sai Fulani kawai.
Bai motsa ba, sai dai ya saki wani murmushin ƙasaita irin na manya, masu kuma ji da girman mulki. Kafin ya ɗago idanunsa ya ɗan dubeta ya ɗauke kansa.
“Wai miyasa ku mata a koda yaushe baku da hangen nesa ne? Yanzu banda dai son neman magana miya kawo zancen haɗa Aina’u da Ramadhan aure? bayan kunji Alhaji Hameed ya zaɓa masa mata…”
“Humm mai-martaba kenan, ni a ganina ai hakan ba wani abu bane, ƙara danƙon zumincine, ka tuna fa Ramadhan shine jikanka na farko namiji a gidan nan, da ace shi ɗin ɗane da namiji ya haifa ba mace ba shine kamarfa magajinka a yanzun, amma sam yaron nan baya son zama cikinmu, akoda yaushe sai dangin ubansa saboda Firdausi ta gama shanyesa su kaɗai yake gani ita da mijinta, amma idan muka haɗashi aure da Aina’u ta tayamu yaƙin jawosa jikinmu ai muma ka…….”
“Ya isa dan ALLAH. Yanzu nan Wasila bana hanaki irin wannan zancen ba? Yanzu miye abin asiri dan Ramadhan yafi buƙatar ya rayu a gidan su?. Karfa ki manta can ɗin shine adonsa, kuma shine tunƙahonsa, to bana son ƙara ji, hakama maganar haɗasa da Aina’u inhar ba sune suka sasanta junansu ba bana buƙatar sake jinta. Dan har abada Alhaji Hameed bazai saka doka na karya masaba koda akan ƴaƴana ne balle jikansa da yake da iko da shi tamkar yanda yake da iko akan mahaifinsa. Kuyi masa fatan alkairi kawai ku tsaya matsayinku”.
Fulani ta taune lip ɗinta da ƙarfi da haƙora kamar zata hudashi, sai dai sanin halin mijin nata yasata sakin ɗan murmushin yaƙe da cewa, “To shikenan ranka ya daɗe, yanda kace ai haka za’ayi insha ALLAH anbar zancen. Dama can rashin zama nayi nazarine akan batun shiyyasa ban fahintaba.”
“Haka nakeso ki kasance. ALLAH yayi muku albarka baki ɗaya”.
Da ƙyar fulani ta daure ta amsa tana haɗiyar zuciya. A ranta ko abubuwa masu yawa take kitsawa gameda kowacce shegiyar yarinyace zata aure mata jika sama taka.

(Hummm Fulani kina kaka inaga gimbiya Su’adah uwar miji. To maji yaya za’a kwashe to😜🏃).

___★____★___

*_BINGO CITY_*

Kallon kallo aka tsaya yi tsakanin Asabe da M. Dauda lokacin da akai kici-ɓus. Dan kuwa dai doctor Shamsu da kansa ya shigo da Aunty Hannah da Asabe, shigowarsu babu jimawa kuma Bappi da su M. Dauda suka dawo ɗakin domin yin sallama da Raudha.
Asabe ce ta fara janye idanunta tana jan tsaki, hakan yasa M. Dauda da jikinsa ke tsuma da sabuwar ƙaunarta matsowa kusa da ita cikin ɗan rawar jiki. “Haba Asabe nine fa Dauda ɗinki, dan ALLAH karkiyi fushi dani wlhy sharrin shaiɗanne”.
Hannunsa dake neman taɓata ta buge tana faɗin “Kaine sheɗan ɗin kanka ai macuci kaw……”
“Mommy Please!!…..”
Raudha ta faɗa tana fashewa da kuka dan tasan komai zai iya faruwa akan iyayenta na raba hali. Asabe zata sake magana Bappi daya fahimci su ɗinne iyayen Raudha ɗin yay saurin dakatar da ita.
“Inaga nan ba wajen magana bane, kamar zaifi muyi haƙuri muje daga waje ko masaukinku ko? Ko kuma mu bari zuwa gobe idan ALLAH ya kaimu…..”
“A’a dan ALLAH ranka ya daɗe gara ayita yau ta ƙare, idan ta bar nan bazata sake yarda na gantaba, zama ta iya sace Aminar daga nan ɗin itama”.
Harara Asabe ta balla masa, sai dai riƙe hannunta da aunty Hannah tayi ya sata yin shiru ta haɗiye abinda taso faɗa.

A tare suk rankaya gidansu Asabe, sai dai Bappi motar Dr Shamsu yabi yace Ramadhan ya koma gida, dan sanda suka fito barci ya samesa yanayi a cikin mota, ya sanshi da barcin wuri, dan shi ƙa’idarsa da tara na dare tayi to ya kwanta kuma. Sai dai kwana biyun nan daya tsinta kansa a NAYA hakan bai kasanceba, shiyyasa daya ɗan kaɗaice sai ya kama barci saboda tsabar buƙatarsa da yake yi.
Rikicewa sosai Hajiyar Birni tayi da ganin Alhaji Hameed Harith Taura har cikin gidanta. Mutumin da bata taɓa tunanin koda ganin motar hawansa ba a hanya balle shi kansa. Babban abinda zai birgeka da shi babu wani damuwa ko tsantsamin gidan tare da shi, hasalima da aka kawo ruwa shine ya fara sha tare da godiya.
Su M. Dauda dai an nutsu saboda hararar da Hajiyar Birni ke antaya musu tamkar ƙwayar idonta zai fito.

“Kuyi haƙuri da lattin zuwan gareku matsayin wanda ƴarku tai kasadar bama kariya. Da farko dai naso ace sai ta samu lafiya zanzo da kaina na kawota gareku nai muku godiya na kuma baku haƙuri. Sai dai an samu akasin hakan a dalilin zuwan waɗan nan bayin ALLAH da ayanzu na fahimci shine mhaifin *Raudhat*. Duk da dai na haɗu da ita mahaifiyarta a aaibiti tun randa abun ya faru, hakama ku da bansan matsayinku garetaba har yanzun. Zanyi amfani da wannan damar domin neman afuwarku, ku gafarceni, da nasan Raudhat zatayi wannan kasadar domin ni tabbas zan dakatar da ita, sai dai masu iya mafana kance ƙaddara ta riga fata, sai muce ALLAH ya bata lafiya ya albarkaci rayuwarta. Ku kuma kuyi haƙuri ku koma tare dan na fahimci baƙwa tare da juna, kuma Raudhat batajin daɗin hakan”.
Kafin kowa yace wani abu hajiyar birni ta amshe zancen cikin washe baki. “Ai muke da godiya ranka ya daɗe, ALLAH ya saka da alkairi bisa kulawar daka nuna akan Raudha, dan bamu taɓa zaton hakan ba. ALLAH ya kara lafiya da nisan kwana. Suko babu sauran aure a tsakaninsu dan saki uku ne yallaɓai……”
M. Dauda yay wata zabura tare da fashewa da kuka. “Ni wlhy ina son matata kuma a bincika ba’a cikin hayyacina na saketaba ranka ya daɗe…”
“Eh wlhy wani malami yace asiri Larai ta maka ai”. M. Gambo ya amshe zancen yana matsar kwalar ƙarya shima. Dan dukansu kowa da abinda ke ransa tsakanin shi da M. Dauda ɗin.
Hajiyar birni ta amshe zancen da faɗin, “ALLAH yayama wannan malami albarka tare da Larai, dan sun taimakeni da suka aikata wannan asiri matsiyaci”.
Kuka M. Dauda ya sake fashewa da shi yana fyatar majina da tsohuwar babbar rigarsa tare da matsawa zai duƙa gaban hajiyar birni ta daka masa tsawa. Itama Asabe miƙewa tai cikin masifa sai dai duk Bappi yay azamar dakatar dasu dan shikam baisan hayaniya a rayuwarsa.
“Inaga dan ALLAH ayi haƙuri tunda dukanmu nan ba yara baneba. Kamar wannan magana tana buƙatar nutsuwa kuma tsakaninku ne. Dama nima akwai abinda ke tafe dani game da Raudhat. Dan tayimin abinda wani mahaluki bai taɓa minba a rayuwa, bani da abinda zan sakanka mata da shi amma ina buƙatar irinta a kusa dani. Ma’ana inason ku bani aurenta dan ALLAH ko ta hanyar hakan zan samu damar kwatanta mata kwatankwacin alkairin data min nima…”
Gaba ɗayansu suka waro idanu a kansa, tare da auna shekarunsa dana Raudha. Cikin rawar baki Asabe tace, “Alhaji kai da kanka?”.
Karon farko ya saki ɗan murmushi domin ganin yanda duk sukai diri-diri, gasu dai a mu’amulat tamkar mutanen banza, ƴarsu kuma nutsatstsiya kamila, amma ashe sun san abinda ya cancanta, amma bara ya sake gwadasu. Numfashi yaja ya fesar da gyara zamansa.
“Eh ni da kaina”.
“Wlhy na baka ranka ya daɗe”
M. Dauda ya faɗa cikin zallo da rawar jiki yana sake gurfana gaban Bappi tamkar mai neman gafara.
Da sauri Asabe ta amshe da, “Nidai dan ALLAH ka gafarceni Alhaji ban amince ba, Raudha bazata auri tsoho sa’an kakanta ba. Son zuciyar da naso tafkawa a baya na biye maka Dauda kan alhaji Maude Dallatu ya kaimu ga zuwa wannan matsayin, yanzu ko na gane gsky mutuncin ƴaƴana da ƙyautata rayuwarsu yafiyemin komai a duniya dan sune gatan wata rana. K….”
“K! Yima mutane shiru!!”.
Hajiyar birni ta faɗa cikin daka tsawar data saka Bappi toshe kunne tilas. Aunty Hannah ma da illahirin jikinta ke rawa tun fara mganar Asabe saurin fincikon Asaben tai baya da faɗin, “Asabe kina da hankali kuwa? Kinsan wanene shi a ƙasar nan?”.
Kuka Asabe ta fashe musu da shi. Cikin matsar kwalla tace, “Adda ni babu ruwan da koshi ɗin wanene. Ina duba rayuwar ƴaƴana ce, bana fatan su tashi a irin tamu rayuwar, fatana suyi ƙyaƙyƙyawar rayuwa bawai ta kuɗi ko son duniya ba. Dan haka ku gafarceni, ko ni akace na auresa yamin tsufa balle Raudha”.
A tare suka hayayyaƙo mata har M. Dauda dake jin a yanzu baya buƙatar lallaɓa Asabe, dan zata masa ƙafar angulu ta kaisa ta barosa. Ganin suna neman harmutsa falon Bappi ya dakatar dasu cikin roƙo. Sai da suka nutsu ya fara magana cike da dattakonsa da kamun kai.
“Lallai wannan baiwar ALLAH ta fiku gaskiya, dan kuwa tayi ƙyaƙyƙyawan hange da iyaye da yawa kan kasayi harma da ƴammatan wannan zamani akan auren wanda yake da manyan shekaru. Lallai ke ɗin uwace ta gari, kuma na gode da yanda kika nuna mutuncin ƴarki da farin cikinta shine gaba a ranki fiye da kuɗi ko wani matsayin da rayuwa ke bama bawa mai ƙarewa. Banzo nan dan na koma da buƙatata ba. Dan haka zan sake roƙonki a karo na biyu. Ina son ki yarje mijinki mahaifin ƴarki ya bama jikana auren ƴarku dan ALLAH badan wani matsayi namu ba ko abinda muke da shi. Domin Raudhat a yanzu tana buƙatar ta samu tsaro kodan rayuwarta dake a cikin haɗari, to zamanta anan tare daku kuma komai zai iya faruwa harya shafeku. Badan mu zamu iya kareta ko hana wani ƙaddara sauka gareta ba, domin muma bayin ALLAH ne kamar ita, kamar kuma ku. Alkairin da taiminne yasa nakejin kwaɗayin ɗaukarta ta zama ɗaya daga cikin family ɗina. Ta kuma haifamin jikoki daga tsatsonta da nake fatan suyi koyi da ƙyawawan halayenta wanda tarihi bazai taɓa gogewaba daga abinda ta aikata na alkairi a gareni”.
A kusan tare duk suka sauke ajiyar zuciya, tare da zubama Asabe ido. Zukatansu har zallo suke nason jin amsar da zata bama Bappin.
Taja kimanin wasu dogayen mintuna tamkar mai nazari kafin ta sauke ajiyar zuciya mai ƙarfi.
“Amma dan ALLAH Baba miyasa bazaka duba akwai tazarar rata tsakanin jikanka da ɗiyata ba…..”
“Babu wani banbanci ɗiyata, domin kuwa dukanmu ALLAH ne ya haliccemu, ya kumace mu bauta masa shi mai rahamane ga duk wanda yayi biyayya ga hakan, sannan mai azaba ne ga duk wanda ya bijire masa. Dan haka ki sani babu wanda yafi wani a gun ALLAH sai wanda yafi jin tsoronsa. Ni da ku da Raudhat duk abu gudane. Mutanene masu barci, masu kashi, masu mantuwa, masu shagala, masu… Masu…. Masu….. Da yawa.”
“Hakane ranka ya daɗe. Na gamsu da bayaninka, zan kuma iya amincewa da buƙatarkane idan har Raudha ta amince da auren jikan naka”.
Babu wanda baija ajiyar zuciya ba a falon, kafin suɗan ƙara tattaunawa da Bappi, daga ƙarshe yay musu sallama suka rakasa har wajen Dr Shamsu dake jiransa a mota dan shi bai shigo ba. Tare da su M. Dauda suka tafi, dan yace zai kama musu masauki tunda nan babu wajen kwana.
Aiko sai murna suke tamkar su ciza uwawunsu dan daɗi😂😝………✍
*_Typing📲_*

 

 

Leave a Comment





No one has commented yet. Be the first!
Leave a Reply