Bakar Inuwa Hausa Novel Hausa Novels

Bakar Inuwa 26


Bakar Inuwa 26
Viral

Episode 26_*

…………A ɓangaren shugaban ƙasa kuwa yana cikin gidan lokacin da aka kawo Raudha, sai dai yana tare da wasu manyan mutanen ƙasar NAYA da sukazo masa gaisuwar barka da shigowa gidan gwamnati. Daga haka suka cigaba da tattauna wasu abubuwa da suka shafi ƙasar tare da shi. Zaman saurarensu kawai yayi da tankaɗa da rai-rayar dukan kalamansu. Alhmdllhi zaman kuwa ya masa daɗi duk da yana buƙatar son kwanciya ya huta, dan ya fahimci abubuwa da dama wanda ada bai kawosu cikin ransa ba.
Bai samu shigowa ba sai kusan ƙarfe ɗaya da rabi na dare, a galabaice yake da son kwanciya da kuma jin yunwa, dan haka ido rufe yashigo ciki batare da tunawa da wanzuwar Raudha matsayin mata kuma amarya a gidan ba.

★★

Hasken ranar daya leƙo ta cikin labulen window ya haske fuskar Raudha ya sata fara motsa idanun da gyar, dan kanta har yanzu ciwo yake mata har a cikin barci. Idanun ta buɗe da ƙyar kuma a hankali, sai dai hasken ya sakata sake maidasu ta rufe sannan ta kare fuskar da hanunta. Sake buɗewar tai duk da nauyin da yay mata. Da ƙyar ta yunƙura ta tashi, tare da bin jikinta da kalllo zuwa ɗakin, ganin time ya sata tashi a zabure ta diro ƙafafunta bisa tattausan lafiyayyen carpet dake gaban gadon. Bata da nutsuwar cigaba da kallo da mamakin ɗakin, ta nufi ƙofar da zuciyarta ke tabbatar mata toilet ne. Ilai kuwa tayi sa’a dan ta dace da hasashenta. Nan ma bata damu da zaman yima komai kallon ƙurilla ba, duk da akwai abubuwan kallon kuwa bila adadin, tai alwala ta fito.

Wata nannauyar ajiyar zuciya ta sauke lokacin data idar da salla. Tsami da ciwon zazzaɓi dake cin ƙashinta ya sata yanke shawarar sake komawa cikin toilet ɗin tayo wanka da ruwa mai ɗumi. Sosai taji daɗin jikinta, sai da ta fito kuma idonta ya raina fata, dan babu kaya ko ɗaya a ɗakin sai na jikinta. Jiri da takeji da rashin mafitar inda zata nema kayan sakawa ya sata faɗawa gadon ta sake kwanciya tare da jan bargo ta ƙudundune. Rawar sanyi ta fara a hankali kafin wani zazzafan zazzaɓi da yafi na daren jiya yay mata rijib.

★★

Tun kammala tsaftar lungu da saƙo na gidan da farar safiya da ma’aikatan gidan sukai shugaban ma’aikata ya tattaro kowa sukai zaman dakon fitowar first lady dinsu domin gabatar mata da kawunansu. Sai dai kuma har kusan goma na safe babu ita babu alamarta. Shugaban ƙasa ko tun bakwai na safe yabi ta sirintacciyar ƙofar da bai zama lallai kowa na gidan ya gansa ba inba wanda suke a harabar gidan ko aiki ta sashen ba ya fita zuwa office.
Basu gaji ba suka cigaba da zama har kusan sha ɗaya, wasu a cikinsu dai sai ƙunkuni suke a zuciya da sukar wulaƙancin first lady, waɗan da suke a gidan tun zamanin tsohon shugaban ƙasa na ayyana (ita kuma da salon wulaƙancin da tazo kenan). Wasu ko masu ɗan hankalin ciki na ayyana maybe ango ya angwance ne har first lady ɗin kuma amarya ta gagara fitowa. Haka dai sukaita tunani barkatai kowa da irin nasa hasashen har su aunty Mariya da sukazo kawo akwatinan lefen Raudha suka iso gidan.

Kusan a tare suka iso da su aunty Hannah da sukazo domin amsa. Sai dai halin da suka iske Raudha a ciki ya sakasu mantawa da wani karɓar lefe ko badawa. Aunty Mariya da tunaninta ya tsaya akan shugaban ƙasa Ramadhan yayi angwancine amma ya tsallake Raudha ya fita sai faɗa takeyi. Dan duk wanda ya dubi yanyin Raudha ɗin, da idanunta da suka koɗe saboda kuka dole kai tsaye ransa ya basa abinda aunty Mariyan ke zargi.
Duk falo suka koma bayan sun mata sannu, aka bar aunty Hannah kawai tare da ita, acewarta zata taimakawa Raudhan ta gyara jikinta. Dan tasan yaran yanzu da son jiki yanzu haka bata shiga ruwan zafi ba.
Kalaman aunty Hannah ba ƙaramin ƙona ran Safina ƙanwar shugaban ƙasa dake bi masa a haihuwa da Aina’u da tazo kallon ƙwaf suke ba. Dan koda akace bara a kimtsa Raudhan Safina ta dubata tunda likita ce, ca tai bata iya duba patient na gida.
Tsaf aunty Mariya ta fahimceta, dan kaf ƴaƴan gimbiy Su’adah idan ka cire Bilkisu da Basma babu mai ƙaunar auren Raudha, saboda gimbiya Su’adah ta gama fallashe musu sirrin asalin Raudha ɗin kaf da cusa musu ƙinta. Su Basma ne kawai basu ɗauki abin da muhimmanci ba. Acewarsu ma ai ba Raudha ɗince ta aikata karuwancin ba. Talauci kuma ba’a goshi yake ba balle a gane wanda ya fito a cikinsa, su dai sun son Raudha kodan taimakon kakansu da tayi wanda da yanzu labarin wani ake bashi ba.
Aunty Mariya tasan yanzu Ramadhan zai musu matuƙar wahalar gani musamman a wannan ranar daya fara shiga office, dan haka tai kiran Anne ta sanar mata suna buƙatar doctor yazo ya duba Raudha ɗin. Anne da zuciyarta ke mata hashe irin na Aunty Mariya cikin damuwa tace, “Ya cutar musu da yarinya ko Mariya?!”.
Cikin jin nauyin Annen Aunty Mariya tace, “Anne sai dai haƙuri, ƴaƴan nan namu na yanzu sam basu da tausayi. Komai yinsa suke da ƙarfin tuwo da tunanin abari ya huce…..”
Ƙwafa Anne tayi cikin takaici ta ballama Shugaban ƙasa Ramadhan da ake kan gaɓar nunawa a television zaune a office suna gaisawa da vice ɗinsa Alhaji Yaro glass harara. “Kai gaka anan hankali kwance kabar ƴar mutane a wahale ja’irin kaya”.
Oho baima san tanaiba, hasalima shi har yanzu bai tuna da wata Raudha ba a ransa. Musamman da tunda yazo office ɗin suna tare ne da vice ɗin nasa, bayan yayi zaman mintuna talatin da wasu manyan mutane. Yayi ƙyau matuƙa cikin shadda kalar ruwan ƙasa mai ɗan duhu kaɗan sai maiƙo take da ɗaukar idanu. Ɗinkin babbar rigane daya kara masa kwarjini da girman shekaru ga mai kallonsa. Fuskarsa tayi fayau saboda ramar da yayi, sai dai wasu kai tsaye suke fassara yanayin cikar haiba da kamalar fuskar tasa da ya sha angwanci ne kawai. Ga hularsa tangaran dake ta ɗaukar idanu na sake fiddo ainahin ƙyawunsa kai tsaye.
Anne ta ɗauke kanta daga kallonsa dai-dai sanda aka sake nuno yana musabaha da Alhaji yaro glass, tsintsiyar hannunsa dake sanye da baƙin agogo da baƙin link mai brown stone suka bayyana. sai zabba na azurfa biyu dake a yataunsa wanda duk itace ta saya masa su a saudia.
“Lafiya wai kiketa sababi ke kaɗai Janna?”.
Dattijo Alhaji Hameed Taura ya faɗa lokacin da yake fitowa daga toilet ɗin bedroom ɗin nasa da Anne ke zaune. Cikin sake ɓata fuska tace, “Da jikanka nake mana”.
“Oh-oh mi yayi ɗan bawan ALLAH ”.
“Kaface haka mana. Yanzu Mariya ta kirani wai a tura musu likita. Yaje ya farma ƴar mutane babu tausayi balle duban ƙarancin shekarunta. Bai kuma tsaya neman mai taimakonta ba ya tsallake ya fita sabgar gabansa shi a dole ga shugaban ƙasa”.
Murmushi mai faɗi Alhaji Hameed yayi yana kaiwa zaune kusa da matar tasa ƴar daru. Ya kamo hanunta cikin nasa idanunsa na yawo a fuskarta. “To amana afuwa dan ALLAH. Insha ALLAH bazamu sake ba”.
“Ko jikina kunne ne ba yarda zan bazaku sake ba. Amma ina gargaɗinku da ku kiyayeni”.
Tai maganar tana tashi da cire hanunta cikin nashi dan ta ɗakko ɗayar wayarta a ɗaki ta kira Doctor. Binta yay da kallo yana dariya ƙasa-ƙasa. Banda dai daru irin nata mutum da matarsa sai a hanashi yin yanda yaso. Shekarar Ramadhan nawa babu aure, kuma shi shaidane Ramadhan baya neman mata tun yana saurayi balle yanzun. Dole kuwa ya damƙi mace a samu matsala.
Bata daɗe da fitaba ta dawo tana sabuwar mitar ƙin samun Doctor Hauwa’u, dan haka ta sake kiran Aunty Mariya taji yaya.
Koda aunty Mariya ta ɗaga saita ce tama kwantar da hankalinta an samu doctor da tazo zata dubata. dan aunty Hannah ta kira wata ƙawarta dake nan kusa da fadar shugaban ƙasar.

Duk da aunty Hannah ta lura zazzaɓi ne kawai da damuwa ke damun Raudha babu wani taɓata da ango yayi saita zaɓi yi musu ƙarya da zaunar dasu akan hasashensu na cewar ai ta gasa Raudha a ruwan zafi, dama batayi bane da ƙyau shiyyasa. Shi kuma shugaban ƙasa yana sauri yaje office bai sake taimka mata ta shiga ba da safen nan.
Kalamanta sun sake baƙanta ran su Safina har Aina’u najan tsaki da hura hanci, zuciyarta kam kamar ta ɓallo ƙirji ta fito dan takaici. Aunty Hannah najin za’a kira doctor daga Taura house tai ruwa tai tsaki akan akwai ƙawarta anan kusa zata kirata basai an saka kowa wahala ba. Ilaiko haka akai, Doctor Farhat tazo ta duba Raudha, ta kuma bata magungunan zazzaɓi harda allura da ledar ruwa ɗaya. Sai suka haɗa baki koda su aunty Mariya suka shigo nuna musu sukai dai har ciwo shugaban ƙasa Ramadhan ya jima Raudha, amma basai anyi ɗinki ba zai warke.
Sosai mamaki ya kashe Raudha a kwance, dan kuwa tanajin lokacin da suke ƙulla zancen a toilet da suka shige, ita kuma ta bisu ta laɓe dan ca take allurar mutuwa zasu mata ma tunda yanzu aunty Hannah ba’abar yarda bace ba. Sai matuƙar kunya ta hanata iya buɗe ido ta kalli kowa a cikinsu duk da addu’oin da suke jera mata na samun lafiya da albarka. Ga wani takaicin aunty Hannah da mamakinta. To miye nayin ƙaryar dan ALLAH anan? Koda ma hakance ta faru sai an fallasata ma duniya da dangin miji.

Har suka bar gidan ran adda Asmah da su Safina a ɓace yake. Aina’u kam ai ba’a magana. Dama can batazo bikin ba jiya ta iso Bingo saboda bikin rantsar da shugaban ƙasa. Yau ko tazo ne danta gansa duk da akwai shakkar hakan tare da ita a dalilin wasan ɓuya da sukeyi ita da shi game da wani al’amari daya faru a america kusan shekara huɗu kenan. Lokacin yana farko-farkon shiga ruɗanin rasa Amnah da Haseenah.

Bayan wucewar su aunty Mariya, Aunty Hannah da aunty Halima suka buɗe akwatunan lefen suka gani. Har cikin rai sai da aunty Hannah taji hassada ta soketa, dan ko ita data ɗauka tsahon shekaru tana kutsetseniya cikin manyan mutane bata taɓa ɗaura wani zanin ba. Kayane masu tsada da ƙyau. Ita kanta gimbiya Su’adah da wannan takaicin masu kawo lefen suka barota. Aunty Halima dai daɗi taji ta kumayi addu’a, dan koba komai uwarsu ɗaya ubansu ɗaya da Asabe. Ballema ita mace ce mai zafi da sauƙi, tana da kirki kuma da son dangi. Gata ƴar gaskiya da gaskiya. Dan tun bayan auren Asabe itama ta fahimci aure shine mutuncin ƴa mace ba rayuwar da mahaifiyarsu ta ɗorasu a kaiba. Batai shawara da kowaba ta nutsu ta tuba, wanda ta tuba dominsa kuma sai ya kawo mata mijin aure cikin sauƙi bisa rahamarsa.
Duk yanda aunty Halima ta hana karsu ɗauki komai aunty Hannah bata saurareta ba. Kowa a gidansu sai da aka ɗaukar masa wani abu a lefen sannan suka wuce bayan sun damƙa Raudha hannun Tambaya wai ta kula da ita idan ta tashi a barci. Aunty halima dai ba haka taso ba, taso suyi haƙuri har Raudha ta farka suji ko tanada buƙatar wani abu, amma babu yanda ta iya tunda aunty Hannah na gaba da ita.

*_TAURA HOUSE_*

A Taura house kuwa sabuwar fitina su Adda Asmah suka sake kunna gimbiya Su’adah. Wani irin zogi takeji a ƙirjinta da jin mai rabata da Ramadhan sai ALLAH……
“Wlhy Ramadhan yaban mamaki, banyi zatoba daga garesa, bansan mi yarinyarnan ta mallaka ba da har ya ruɗesa da kusantar ta….”
A hasale Fulani dake shirye-shiryen komawa masarauta saboda kiran da mai-martaba ya mata tazo ta tare gidan surukai ta katse Adda Asmah mai maganar a hasale. “Aiko yayi na farko yayi na ƙarshe dan ubansa. Bandama namiji duk inda yake maye ne (ba ni na faɗaba fulani ce😱) har miye a jikin yarinyarnan na bibiya. Yayta wani ɗaga kai da izzar banza a waje ashe shashasha ne”.
Cikin taɓe baki Addah Asmah tace,
“Ammy shiyyasa tun jiya nace a fara bata maganin nan na hana ɗaukar ciki ai, shima muyi masa gargaɗin karya raɓu yarinyarnan dan nidai nasan yanda Ramadhan ya jima babu mace koda bai son yarinyarnan zaiyi ruwan kashe gobara da ita. Amma sai kukace babu abinda zaiyi da ita. A tunaninku yanda take ƙyaƙyƙyawa ɗin nan zai iya kauda kansa gareta tunda ma ba tabbacin baya sontane damu ba……”
Gimbiya Su’adah ta haɗiye wasu hawayen baƙin ciki dake neman zubo mata. Cikin kaushin murya da jin tsananin sakejin sabuwar tsanar Raudha ta katse yayar tata, “Aiko zaiyi aman abinda ya taɓo dan ubansa. Itako sai na maida rayuwarta abin tausayi a ƙasarnan itada karuwan dangin uwarta da faƙiran dangin ubanta. Shiko zaiyi nadamar haɗa shimfiɗa da ita da yay, zaizo ya sameni ai”.
Kuka Aina’u ta sake fashewa da shi dan duk suna zaune a falon ita da su Safina. Basma da Bilkisu ne kawai babu. Lubnah dake bima Safina kam tafi kowa ɗaukar zafi, dan halinta kaf irin na gimbiya Su’adah ne dama. Rashin son Raudha ya hanata zuwa fadar shugaban ƙasar tun jiya.
Cikin takaici Munirah dake bima Bilkisu ta harari Aina’u. “Wlhy aunty Aina kina bada mata. Miye abin kuka dan Yaya Ramadhan ya kwanta da waccan wawuyar yarinyar. Nifa kune kuke ganin laifinsa Maa. Karfa ku manta jinin karuwaice, wama ya sani ko itace taja ra’ayinsa ga hakan tunda iyayenta sun koya mata. Kuma koba komai ya mora sadakinsa da wahalar da aka sakashi yakeyi na yawon zuwa ƙauye da kisan kuɗi. Ni dama ya farka shegiya yanda bazata ɗinku ba mtsoww!!”.
Duk da kasancewar Muneera ƙaramar yarinya a cikinsu sai maganarta tai musu daɗi, dan daga Yusrah sai auta Basma a ɗakin Gimbiya Su’adah, a yanzu hakan shekarun Muneera gaba ɗaya bai wuce ashirin da ɗaya ba zuwa da biyu. Amma har take iya waɗannan zantukan.
Safina ta ɗanyi dariya, “ALLAH kumafa zancen Muneera haka yake, baima kamata muga laifin Brother ba. Dan haka kibarma fushi da shi Maah. Yarinyar zamu cima ƙaniya kawai. A kuma ɗorata akan maganin hana daukar cikin nan da lalata mahaifarta. Sannan tunda Muneera ta kammala karatunta ta koma can da zama ita da Lubnah, sune zasuci mana ubanta cikin sauƙi kuma suna kawo miki abinda duk ke faruwa a gidan.”
“Shawararki yayi dai-dai Safina”. Fulani ta faɗa cike da isa da ƙasaita. batare da ta basu damar cewa wani abuba ta cigaba da faɗin, “Harma da Aina’u. Tsakanin Bilkisu da Basma ma wata taje su haɗu su zauna”.
Adda Asmah tace, “Eh hakan yayi Ammy. Sai dai kinsan Halin Ramadhan zai iya cewa sunyi yawa. Kodai su Bilkisun su zauna su”.
“Aiba lokaci ɗaya zasu tafi ba, da daɗɗaya kodan waɗan can tsoffin suma da basa iya gani su ƙyale. Amma zuwa Basma ko Bilkisu nada nasa amfanin. Su nuna suna sonta suke, zatafi sakin jiki da su har su san komai nata. Su kuma su Lubnah ta hanyarsu zasu dinga sanin wasu abubuwan ai ko”.
Cikin gamsuwa suke jinjinama Fulani kawunansu. Banda gimbiya Su’adah da har yanzu zuciyarta ke a matuƙar ƙuntace. Dan ko magana bata iya sakeyi ba.

____________________

A can bangaren su Aunty Hannah ma suna zuwa rabon ganima aka fara, sai dai banda Asabe da tausayin ɗiyarta ya rufeta game da labarin da aunty Halima ta bata dan itama batasan ba gaskiya bane tunda aunty Hannah bata sanar mata ba. Taji inama Raudha nada waya yau data kira taji ko muryartane taji sanyi. Dan rabonta da ita tun randa aka ɗakkota da ga Hutawa. Ita nan gida tayo dama ita da hajiyar birni. Su aunty Halima ne kawai suka je kai amarya………✍

 

*_Hummm🚶🏻_*

________________________

Duk wacce batayi anfani da sabulunnan ba anbarta abaya acan karshen bayama kuwa duk Mai tantama akan sabulai nagyaranjiki cewa basa Aiki toh yacire mg’s domin kankat ne insha Allah babu Wanda yayi anfani dasabulunmu yace baiyi ba koyaushe mg’s sai sanbarka amare da uwargidaye hardama yanmata kuhanzarta kusamu naku ba karya domin bama cika Baki kugwada kubada labari da bakunanku sabulu daya tamkar dubu wadandama basasan using cream sabulun mg’s herbal whitening black soap yawadacemuku jikinku zaiyi kyau koyaushe kukasance clean cikin kamshi Kuna glowing koda bakusa turare ba🤗

Kayanmu bana bleaching bn organic ne sunagyarajiki fiye da tsammaninku zaifiddomuku da ainihin natural beauty dinkine Wanda yagwada shi zaitabbar amare kuyi kokari kumallaki mg’s domin baruwanku da zuwa adirjemuku jiki zakuga yanda fatarku zata dinga walwali
Ina masu pimples
Tabo(spot)
Sunburn dama dukwani matsalar fata kuyi kokari kunemi soap dinnan before 2weeks zaisharemuku hawaye kuzama abun kwatance
Sister’s masu nankarwa kuma kunemi soap dinnan Yana rage nankarwa sosai🧖🏻‍♀️duk me shakku tayi kokari tagwada mg’s insha Allah bazakiso rabuwa dashi ba

Akwai maisa haske Amma kayanmu nafada bana bleaching bn zaifiddomiki d ainihin halittarkine yagoge dukkan dattin jiki

Akwai Kuma Wanda zaimiki maintaining skin dinki yasaki fresh fatanki tazama kalar hutu

Pls bamacika Baki you HV to try it and see for yourself
100%tested nd trusted

Soap price:3k
Location:kaduna buh munaturawa ko Ina Amma delivery is not free

Maiso kindly message 08062991549
07046881166
Call 08064532391

Note:Babu inda zakusami mg’s herbal whitening black soap sai a number dinnan bairiga yakai market b inyakai we will let you know buh as for now wnn numbern ne kawai🙏

Maiso yahanzarta before yaji sold out akwaisu available now insunkare you HV to wait akawo so maiso yahanzarta🙏adade anayi sai gsky🤭🤝

Mg’s skincare

_________________________

*_ZAFAFA BIYAR (5) ZAZZAFAR TAFIYA🔥🔥👇👇👇_*

*1*~ *_KUFAN WUTA_*🔥
_Safiyya Huguma_

*1*~ *_BAQAR INUWA_*💥
_Billyn Abdul_

*1*~ *_RAYUWAR MACE_*💅
_Hafsat Rano_

*1*~ *_MASARAUTA_*💪
_Miss Xoxo_

*1*~ *_NOOR ALBI_*❤‍🔥
_Mamuhgee_

 

Guda 1👉300
Guda 2👉400
Guda 3👉500
Guda 4👉700
Guda 5👉1k

*_ZAKU BIYA KUDINKU ANAN👇👇_*

Bilkisu Ibrahim Musa
1487616276
Access bank

Number shaidar biya👇🏼

*_09032345899_*

*KATIN MTN*👇👇

09166221261
__________________

*_JAMA’AR JIGER zaku iya biyan kuɗin littatafan ZAFAFA BIYAR kuma ta nan👇🏼_*

 

Guda daya=300F
Guda biyu=400F
Uku=500F
Hudu=700F
Biyar=1000F

*ZAKU TURA KATIN WAYA NA (MOOV ko AIRTEL) ZUWA WANNAN NUMBER,TARE DA SHAIDAR BIYA*👇🏼

+227 95 16 61 77

 

*_TEAM ZAFAFABIYAR🔥🔥🔥🔥_*

_____________________

*_BAƘAR INUWA…👇🏻_*

Da ɗumi-ɗuminsa💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻

Please
*_Follow me_*
*_Share_*
*_Comments_* akan abinda ya shige maka duhu.

_AREWABOOKS, dan zaku dinga samun sabbin pages galla-galla akan lokaci insha ALLAH. Maza garzaya ka karanta naka hankali kwance. Ka kuma yi following ɗina ko dan kar ayi babu kai, da a baka labari gwara ka bayar🥰🥰🤝🏻👇🏻_

*YADDA AKE BUƊE ACCOUNT A AREWABOOKS*

Bayan kaje play store ka ɗakko ya sauka a kan wayarka. Za’a cike Form ɗin kamar haka: –

*Enter your name:* (Cikakken sunanki)

*Enter your mail:* (Email ɗinki)

*Enter an username* (Sunanki)

*Enter your password:* ( misali 12341234)

*Confirm password:* (misali 12341234)

Sai a taɓa *Sign Up* shikenan an buɗe account a ArewaBooks💃🏻😂.

*Continue with Google* – Idan kana da gmail/email akan wayarka kawai Continue with Google za’a taɓa zata buɗe maka account a ArewaBooks kaitsaye.

*Register* – Shine cike form domin buɗe account a ArewaBooks.

*_AREWABOOKS LINK kai tsaye_*

https://arewabooks.com/book?id=620032232dff83519bbad5a3

Masu iPhone

Zaku iya bibiyar shafinmu
https://arewabooks.com

*_Kuzo mu haɗa ƙarfi da ƙarfe domin gyara tafiyarmu. Koba komai ɗan uwanmu ne bahaushe ya zauna ya tsara ya kuma buɗe App… Ɗin domin cigabanmu da jin daɗinmu. Wannan abin alfaharine_.*

*_MARUBUTA DAKE NEMAN ƘARIN BAYANI KO MASU KARATUN MA, ZAKU IYA NEMANMU TA WANNAN NUMBER_*

+234 903 177 4742

_Alkairin ALLAH yakai gareku masoya a duk inda kuke, tare da fatan alkairi muna sonku irin trillions ɗin nan😍😘😍🥰😍😊_.

 

*_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻_*

*_Typing📲_*

 

 

Leave a Comment





No one has commented yet. Be the first!
Leave a Reply