Bibiyata Akeyi Hausa Novel Hausa Novels

Bibiyata Akeyi 6


Bibiyata Akeyi 6
Viral

Page 6

Sorry for the last Page there are some several mistakes wllhy bansamu nagyaraba.

*
Jiyayi andafashi saurin juyowa yayi, nan take kuma kunya ta lullubeshi, ya mahmood ya kamashi yana tsare masa kanwar mata da idoh,

Karasowa tayi tajama amal kujera tazauna sannan itama tazauna, dama kujeran dining din mai kujeru shidane, anty nazaune kusada yah mahood, najeeb kuma yana dayan gefen ya mahmood itakuma tasa amal atsakiyanta da najeeb,

Anty tatashi tafara saving dinsu tana bude food flask din wani kamshi yadaki hancinsu lumshe ido najeeb yayi sannan yabudesu, saukesu yayi akan *hanna* wadda ita batasanma yanayiba, dan tunda ta iso tadauke idanta daga kansa,
Anty ne data zubawa amal abinci saurin rike hannun anty anty tayi, owh owh nibake dakiyi saving dinaba ni ummah ne data zubamin, ohoh kyaji dashi keda ummankin,

Juyawa tayi wajan najeeb daniyar zuba masa saurin langabar da kansa gefe yayi sannan yace owh owh nibake daki zubamin ba ummane data zubamin yakwaikwayi maganan amal amma kuma harcikin ransa yafiso tazuba masa, wata harara tawatsa masa kamar idanunta dasu fadi kasa, idoh daya ya kanne mata tare dayin murmushin dashikadae yasan ma’anarsa,

Juyawa anty tayi ta kalleta, maza tashi kizuba muku abinci, batareda tayi wani tunani ba dan Azatonta koh yabi maganar amal ne kawae, shikuwa yaya mahmood yagama gane yanda yadosa,
Idan haka tafaru bakaramin farinciki zaiyiba dan yafi kowa yawa kaninsa addu’ar samun mace tagaari, fatanshi kawae Allah yasa bata tsayarda miji ba,

Kunkuni tatashi tanayi ciki ciki tamikawa anty bashir, no kawoshi haka nan muryar najeeb takatseta, yitayi kamar bataji shiba takara mikawa anty yaron wae bakiji mai akafada miki bane, kibashi yaron turo baki tayi, sannan tanufeshi ta dangwara masa yaron, akan cinyarsa, anty baki kawae tasake tana kallon ikon Allah,
Idan kingama shirmenda kikeyi saiki zuba muku abinci, kara turo dan bakinta tayi,
Wani irin kyau yaga tamasa tashi daya tsikar jikinsa tazuba, gashinda ke kwance ahannayensa suka tashi, Jiyayi kaman yaje yayi kissing din bakinta dan yanda take turoshi bakaramin kyau tayiba, saida shi Allah yayishi bameson taba matar daba muharramarsa bace, with time yafada acikin ransa dan duk randa Allah ya mallaka masa ita amatsayin mata wannan dan karamin bakinnata daga ranan bazai kara yin tsauri mawaniva,

Zuba masa abincinda tafarayi ne yadawo dashi daga tunanin daya wulla, zuba masa tagamayi sannan takoma kan amal itama tazuba nata tazauna,

===============

Inah mukabar masu *bibiyan* *hanna* ne tun fitarta daga gida suka fara binta har tashiga lectures tafito, fitarta daga lecture zuwa shop duk lokacin suna bib *bibiyarta* Bayan takarasa shop ne daya daga cikinsu fitsari ya mugun kamashi, dama kunsan ance tsautsayi baya wuce ranarsa domin oppotunity come at onces just like mistake come at onces either dakadauki tsaawon shekaru kana kare abu but na lokaci guda kayi sake da wannan kariyar wannan mistake din da za’asamu ayan secound itx really hard to make it up,

Fitsarine sosai yarikeshi wanda bazai iya jiraba gawajen wajen wucewar jama’a balle yayi awajan, yabukaci dayan dayakai shi yayi aiba wata damuwa tunda akwae mutane ashop tun har dasu dawo kafin asallameta,

Rakashi yayi kafin sudawo abinda suke gudu ya auku wandasu basuda masaniya akan faruwar hakanma domin alokacin najeeb yabige hanna haryaji zuciyarsa takamu da sanda, itama hakanne tafaru awajanta luv at first side,

Dawowarsu yayi daidai da fitowarta daga shop din, nan sukaci gaba da binta, wanda saken dasukayi nayan wannan minute din yana daidai darasa rayuwarsu,

Harzuwa lokacin da tajuya me keke napep zuwa gidan antynta harnan suna biye da ita sanda tazo gidanne ta shiga sukuma sukayi parking car dinsu, sunajiran fitanta,

Koda lokacin da najeeb yashigo tareda yaya mahmood yazo wanda yaje hargida yadaukeshi kuma sunriga da sunsan motar yaya mahmood kuma sunsan matsayinsa a wajanta so basu damu daduba motarshi ba koda wani acikinta dake motan nada bakin tinted,

Haka yayita kallon ta harsuka karasa cin abuncin, anty amma kin iya abinci wallahi nima Allah ya bani wacce ta iya girki yafadi haka tareda satan kallanta ta kasan idoh, to Ai baninayi ba cikin zumudi yace wayayi gata Zaune kusa dakai, hmmm yaja gauron numfashi anty amma mijinta yayi sa’a sainaji dama nine wannan mai sa’ar,

Siririn tsaki taja kaifa kafara wuce gona da iri ha’ah ta murguda masa baki, wow😍 gaskiya fushi yana miki kyau kamar karkiyi dariya,hakan dayafada ne yasata murmusawa wow to Ai kuma dariyan yafi miki kyau kainama kasa tantancewa

Ahaka yayita jan ta da kalamai masu dadin sauraro harta bashi phone number dinta,
Saida tayi la’asar kafin tafara shirin tafiya,
Bayanda bayiba akan yasauketa agidah amma fir taki,
Haka sukayi sallama da anty kafin tafuto da niyyar wucewa gida batayi mamakin ganin motarsu,
Sanda tayi dan tafiya kafin tasamu abin hawa gida tawuce,

DUBAI

Major general MG Abudullahi ne Zaune a office gabaki daya tunda karfe 11:30 tabuga a agogon nigeria wadda yayi daidai da 2:30 a agogon akasar dubai wani irin faduwa gabansa keyi kuma yarasa dalili tunyana daurewa avun har zazzabi yake shirin sa masa ba shiri yabaro office yayi gida amma duk da haka yakasa samun nutsuwa kamar wanda wani mummunan lamari ke shirin faruwa dashi,
Captain ahmad yafada cikin dagun murya cikin tsafin nama wani dan saurayi wanda bazaifi kimanin shekaru 30 ba ya isoh wajen cikin girmamawa yace Gani yallabai yisauri kakiramin Captain bala jiki harayana bari yaciro waya a aljihunsa dan yasan halin ogannasa bayasan wasa barinma daya fahimci ransa yana bace, ringing daya akadauki wZ33iiyyb3rw3rikawa MG wayan yayi ya karba tareda karawa a kunnensa…..

To be continue

Ur’s
Z33yyb3rw3r

BIBIYATA AKEYI

Bismillahirahmanirrahim

Writting by
Zaynab Bawa (Z33iiyyb3rw3r)

_This Page is sincrely dedicated to u My dear *Ayeshert* *Aly* *garkuwa* u r such a wonderfull person i want u to know that u r _amazing_ so _much_ _love u_

Leave a Comment





No one has commented yet. Be the first!
Leave a Reply