Dare Daya Hausa Novel Hausa Novels

Dare Daya 39-40


Dare Daya 39-40
Viral

PAGE 39&40

 

A hankali momma ta fara magana gaba ɗaya jikinta yayi sanyi tana mugun jin kunyar malam Kamalu da Jameel da yake girmama ta, ina roƙon ka yafemin malam Kamalu, dan Allah kayi haƙuri ka yayimin afuwa ka yafemin, kuma ina neman wata alfarma a gunka dan Allah karka rabani da MAHELET ka barta a guna har lokacin da zatayi aure ko nace harna aurar da ita, girgiza kai malam Kamalu yayi yana cewa ni ban ƙullaci kowa ba a zuciya ta sbd nine mai laifi nine na kawo son zuciya da ƙwaɗayin abun duniya Allah ya yafe mana baki ɗaya sulalewa Abbas yayi yabar falon ya bazama neman HAFSAT cikin gidan babu inda bai duba ba amma bai ganta bah sosai zuciyar sa ke lugude tana buga kardai tafita tabar gidan zai jiuya ya buɗe ƙofar kitchen yaji muryarta tana kuka ƙasa ƙasa hmmm ya sauke ajiyar zuciya, zaune take ta tura kanta cikin kafafunta kamar wata snail duk ta takure guri ɗaya, sosai Abbas kejin kukan har cikin zuciyar a hankali ya ƙarasa gunta yana kiran sunanta Hafsa bata amsaba kuma bata dena kukan bah hannu yasa ya ciro kanta yana ƙarewa fuskanta kallo ya Allah ya furta a fili yana ƙokarin janta a jikinsa fisgewa tayi tana ƙokarin tashi jiri ya ƙara ɗiban ta tayi baya zata faɗi da sauri ya taro ta yana cewa Hafsa wai miye haka, bakiji mai MAHELET ta gaya miki bah kowane bawa fah dakike gani da kalar tasa jarabawa kuma da kalar tasa qaddarar rayuwa. Aekuwa kamar karyayi magana ta fashe masa da kuka janyota yayi ya manna ta a kirjinsa yana shafa bayan ta a hankali a hankali sai sheshekar kuka take haɗe da sauke ajiyar zuciya Fitowar umma kenan da Momma idanunsu suka sauka akan hafsa da Abbas ya rungumeta tsam a ƙirjinsa tayi lamo sai famanshafa bayan ta yake yana magana ƙasa ƙasa bakinsa kawai ne sukaga yana motsi da sauri umma ta dauke kanta saɓanin momma datayi gyaran murya da sauri Hafsa ta raba jikinsu tana komawa bayan sa, batama son ganin waye yayi gyaran muryar kar ace umma ce, sosa ƙeya Abbas yayi yana cewa momma bazaku tsaya ba kuyi dinner anan naga yamma tayi yanzu za’a tayar da sallah murmushi tayi tana cewa MAHELET ce ko Hafsa a bayanka, murmushi yayi yana ƙokarin janyo Hafsa data riƙe masa riga gam ta baya, aekuwa kamar jira take ta fashe masa da kuka tana tirjewa girgiza kai momma tayi, gaba ɗaya komi nasu kala ɗaya ta faɗa a fili tana nufar ɗakin da umma ta shiga saida ta shige yasa hannu ya janyo ta da ƙarfi yana cewa matsoraciya kawai ƙasa tayi da kanta tana wasa da fingers dinta farare tas dasu babu jan lalle akansu sai sheƙi suke suna daukar ido, hannu yasa ya kama hannunta yajata ya nufi wani corido da ita suna kaiwa ƙwaridon ya saki hannunta yana matsawa jikinta taringa yin baya baya har takai jikin bango hannu yasa a samanta yayi mata rumfa a hankali ya kira sunanta Hafsat, Na’am cikin rawar murya ta amsa hannu yasa ya ɗago haɓarta kafin yace please ki manta komi dan Allah banaso wannan abun daya faru ya shafi lafiyar ki, kuma Inaso kiyafewa Baba, baba yana sonku sosai kawai sharrin shaiɗan ne ƙara matso da fuskar sa yayi daf da tata yana shaqar numfashi ta, itama tana shaƙar numfashisa unexpected taji ya manna mata kiss a saman idonta sbd ta rufe idonta gam a hankali yace I Love you, inason ki Hafsa tun ranar dana fara ganin ki naji ina sonki, sosai takejin maganganunsa na shiga cikin zuciyar ta, ƙara matsota yayi ƙadan bcos he wanted to kiss her lip, ta fara mutsu mutsu, aekuwa ya dauki left hand dinsa ya daura kan cikinta, a hankali yace kinci abincin rana kuwa girgiza masa kai tayi sbd jin yanda yake shafa cikin sai yayi ƙasa kamar zai kai kan marar ta sai yayi sama zuwa kirjinta idonta a rufe riffff murmushin gefen baki Abbas ya saki ya fara kokarin haɗe bakinsu girgiza masa kai ta shiga yi, hannuwansa yasa duka biyu ya riƙe kanta ya shiga sakar mata hot kiss a labɓanta yana tsotsar su kamar ya samu sweet, nan take jikin hafsa ya fara rawa kafafunta sukayi sanyi tayi ƙasa tana ƙokarin zubewa yayi sauri taro ta yana zare bakinsa daga cikin nata sbd ya bata damar numfashi, da ɗan sauran ƙarfin da ya rage mata a jiki ta turasa gefe ta fara ƙokarin fita daga corido din yabi ass dinta da kallo tafiya take a natse amma duk tako ɗaya idan tayi sai sun motsa kamar ita ke jiuyasu, cije lips din sa na ƙasa yayi yana shafa gemunsa saida ta jima sosai da fita kafin ya fito ya nufi part dinsu alwala ya dauro ya nufi masallaci har ana ƙokarin tayar da sallah koda ya shiga da ido Dr Jameel ya bisa sbd ganin yanda yake ta faman murmushi, Saida sukayi sallar isha’i kafin gaba ɗayasu suka nufi gida Dr Jameel da Abbas sune a gaba sai Abba da Baba suna baya sosai a hankali Abba yace malam dan Allah kayimin wata alfarma Inaso ka baya yarana Abbas da Dr Jameel auren yaranka Dr Jameel ya nuna yana son MAHELET Hakama Abbas ya nuna yana son hafsa tun ranar da ya tsinto ta a hanyarsa ta zuwa bungudu shiru Baba yayi kamar bazaiyi magana bah sai kuma yace bakomi Abba Allah ubangiji ya tabbatar mana da alkhairi, Ameen Abba yace yana jin mugun daɗi a ransa, koda suka isa gida Umma da Momma suna zaune a falo akan 3siter sai MAHELET da HAFSAT akan 2siter, Abbas da Dr Jameel suna zaune akan 2siter dake kallon su MAHELET kasan cewar set 2 ne na kujeru a falon kuma babban falo ne sosai, su Abba suka shigo bakinsu dauke da sallama gaba ɗaya suka haɗa baki gurin amsawa saɓanin HAFSAT dako ɗagowa bata yi ba bare taga masu sallmar duda ta riga tasan masu sallamar. Gaishe su sukayi suma suka samu guri suka zauna aka dan taɓa fira kaɗan Kafin umma ta miƙe tsaye tana cewa bara na kawo mana abincin anan sai muci Hafsa na ganin ta nufi darning itama ta miƙe domin ta taya ƙwaso wasu kayan MAHELET na zaune sai latsar waya take bama tasan su umma sun tashiba a hankali momma ta kira sunanta tana cewa MAHELET ki ajiye wayar nan ki tashi ki taya umma ta hafsa haɗo kayan abinci ɗago kai tayi aekuwa idonta ya sauka akan na Dr Jameel ya ɓalla mata harara tashi tayi ta ajiye wayar akan cinyar momma ta nufi darning itama haka suka tattaro komi na abinci da aka tanada da abunsha suka jerasu a falon akan babban carpet, umma ta shiga zubawa kowa Hafsa ita kuma tana dauka tana daurawa kowa a gabansa taje ajewa Abbas yabita da kallo idonsa ya sauka akan kirjinta da yake iya hangowa ta saman rigar ta masha Allah ya furta ganin yanda suke shining, harta ajiye abincin tabar gun baisani, girgiza kai umma tayi tana mugun tausayin Abbas ganin yanda ta mutu son Hafsa tana yimasa addu’ar Allah yasa shima hafsa ta sosai kamar yanda yake son ta, Haka suka fara cin abinci sunaci suna taɓa fira kaɗan kaɗan, ƙarfe tara suka gama cin abinci Momma da MAHELET sukayi shirin komawa gida Driver akasa ya mayar dasu Abbas shi kuma yaja motar momma har suka isa gida. Ya rage daga Umma sai Abba da Baba a falo tuni hafsat ta tashi ta shige ɗaki a hankali Abba yace Hajiya munyi magana da Baba cewa da malam Kamalu Insha Allah zamu sa ranar bukin yaran nan nan bada jimawa ba ni banama son ya wuce satin nan yau Laraba Inaso Insha Allah ranar friday a daura aure saiki gayawa Hajiya Asiya inaji tasan Dr Jameel yana soyayya da MAHELET, ehh ina tunanin ta sani, okay toh dan Allah ki sanar da ita ni zanyi magana da Alhaji Ibrahim Tau Insha Allah haka umma ta tashi tashiga daga ciki Abba da Baba suka taɓa hira ƙarfe goma Abba yakai Baba makwancinsa sukayi sallama,……….✍🏻
[7/27, 8:47 PM] Typing….✍🏻: BONUS PAGE💃🏼💃🏼💃🏼

Leave a Comment





No one has commented yet. Be the first!
Leave a Reply