Hausa Novels Sakon So Hausa Novel

Sakon So 10


Sakon So 10
Viral

EPISODE 🔟

Zaro idanu Principal tayi ganin yanda suka watsa mata drinks sun mata wanka sun bata mata jiki gabaki daya tace “what in God’s name is this Kola and co?” Da sauri duk suka wurgad da gorunan kasa, Principal tace “to disciplinary office now!” dasauri suka fita sannan takalli Lujain wani irin kallo da Lujain takasa fassarawa koname tace “come with me” ahankali ta tsugunna ta dauki jakanta dake tsiyaya da drink ta kakkabe jikinta tabi bayan principal faran safan kafanta har tusan ruwa yake sabida yanda drinks suka jikashi teachers nasu na kallonta wani kalan kallo tawucesu ahankali suka rufamata baya suna fitowa taga student an taruuuu kawai kallonta akeyi kaman yau aka fara ganinta a school din aka wuce da ita saikuma chan taji student na murmuring “God forbid, ewwww wasu na cewa na karuwa” har zuwa office na principal suka shiga principal ta zauna akan wani kujera tanuna mata wani waje teachers kuma suka fita, anatse principal din na kallonta tace “a ina kikasan Alhaji Imran”? Zaro idanu tayi tace “na’am waye Alhaji Imran”? Dan to be honest bamata gane kan maganan ba, ahankali Principal tace “mai company ceramic, at first da aka fara fadamini awaya I thought maybe forcing naki yayi he took advantage of you but after watching the video…….” Principal tai shiru daga gani kasan maganan namata nauyi tace “after watching the video I understood komi yafaru ne with your consent dan is so obvious, ni baran wani iya cewa komiba dan you have your rights as an adult data wuce 18yrs you are 19, keba minor bace, all I will say is have this” tamika mata wani takarda ahankali Lujain tasa hannu takarba ganin letter na susupension yasa dasauri takalli principal din, Principal tace “I believe guardians naki are on their way right now tun dazu muka kirasu wata tsohuwa da farko damuka kira mukaji, hakan yasa muka dauki second number wanda yacemana shine mahaifinki yana hanya” shiru Lujain tayi kawai tana kallon letter ita she don’t even know what’s happening.

Suna parking Gwaggo data gama rudewa tace “Ya ubangiji kasa ba ciwon yarinyar nan bane yatashi ba Wanan damai makarantan takirani gabaki daya” fitowa Baba yayi tareda Mama dasukai gaba daidai lokacin wayan Baba yahau ringing anatse yace “eh muna makarantan yanzu, tom saikun karaso” dasauri Gwaggo tace “waye?” Ahankali yace “Abdulhadi da Yusufa ne” fashewa da kuka Gwaggo tayi tace “kafadamin gaskiya kodai Lujain dina tamutu ne wanan dahar ka kira kannenka suzo nan iyye kafadamin gaskiya” ja idanun Baba sukayi yakalli Mama yace “kujirani anan bari na shiga” Gwaggo na kuka sosai tace “wlh kafanka kafana kaida matanka damai makarantan kunki fadamin abinda ke faruwa saikuma kuhanani shiga wlh saina shiga” dan jim Baba yayi yana kallonta saikuma yace “muje” dasauri Gwaggo tabishi tana goge hawayenta da bakin zaninta data warware har zuwa principal office suka shiga, ganin Lujain zaune nata kallon takardan da aka bata yasa ta taho dagudu tana shafa fuskanta tana bude mata idanu tabude bakinta tana kallon da duba harshenta danta gane ko rashin lafiya take tace “Alhamdulillah babu abinda yasameki yarnan Iyyee Alhamdulillah wayyo Allah zuciyata kubani ruwa Insha” dasauri principal tabata ruwan gora budewa Gwaggo tayi ta kwankwade tass sannan ta zauna Baba batare daya kalli Lujain ba yace “gamu principal” ahankali tace “ba babanki takardan Lujain” ahankali Lujain tamikama Baba takardan fuskanta yakalla da jikinta daya baci da drinks da jakanta dahar lokacin na diddigan ruwa sannan yasa hannunshi ya amsa ya karanta yakalli principal din harzaiyi magana saikuma yatashi tareda kama hannun Lujain yace “muje” tashi principal din tayi tace “kuyakuri sir bazan iya barin yarinyar ku tacigaba da karatu anan makarantan nan ba she is a bad influence zata batamini sauran dalibai kuya kuri babu abinda zan iya” sai alokacin Baba yakalleta yace “akwai abubuwa da yawa da zaki iya na farko shine kare hakkinta jibi yanda akama y’ata wanka da drinks sabida kunga batada kani ko Yaya amakaranta kobaki koreta bama nixan cireta daga makarantan, inaso kisan abu daya, akwai Allah! Sannan zai wanke mini diyata agaban kowa muna nan zakusan you all have wronged her” yaja hannun Lujain dasauri suka fita tashi Gwaggo tayi tana kallon Mama tace “ke Maman su Samira me akace tayi ne kifadamin” chak Mama ta tsaya kaman jira take tace “yarinyan dakike mana tunkaho da ita kina fifitata kan nawa yaran video dinta dawani kato dasukaje excursion akafaninshi na yawo a yanar gizo suna fasikanci sun shiga bayi yana dugurguzanta diyarki na ihun dadi” wani kalan zaro idanu Gwaggo tayi tace “mene shairin kine dai ko” wayanta Mama taciro anan office an principal takunnama Gwaggo video tundaga lokaci da Abee ke kokarin kwance belt har zuwa lokacin daya shiga bayi ga muryan Lujain nan dako amarfi tasani tai ihu wayyooo saikuma uhmmm Uhmm uhmmm saikuma chan aka nuno Laujain tafito corridor tana gyara riganta tajuya dasauri ta tafi tunda Gwaggo take bata tabajin tashin hankali hakaba baya tayi zata sume dasauri Mama ta tarota tace “ni kada ki sumemin yace dagangan na nuna miki inason kashemai uwa mutafi” takama hannun Gwaggo tanaja suka fita awaje taga duka yaranta da Yusuf da Abdulhadi dukansu suna sanye da manyan kaya sai Yayanta sunyi jugum suna kallon Lujain da idanunta sunyi ja ganin Gwaggo tafito anriketa yasa tai wajen Gwaggo da sauri saiga hawaye, zaunawa Gwaggo tayi akasa tana zaunar da Lujain bata damu da yan makaranta ba tanuna kanta tace “Lulu tun kina cikin kwalban asibiti nake rainanki nasanki ciki da bai nasan halinki tsaf amman bansan ki da Iskanci ba kifadamin gaskiya meyamiki kike ihu” zaro idanu tayi dukta rude tace “waye? Wani ihu Gwaggo”? Wani kalan fizgota Baba yayi cikin ihu kaman zai mareta yace “ranan dakukaje excursion me mutumin nan yamiki abayi kike ihu”? Jikinta har rawa yake ganin Baba na shirin dukanta tafashe da kuka tace “wlh babu komi Baba” Baba Abdulhadi yace “to ubanme aka miki kike ihu”? Cikin kuka sosai tace “Baffa wlh naje bayi na kalli video wan nan dan kwallon Mandawari ne awaya” kusan dukansu atare sukace “a ina kika sami waya”? Cikin kuka sosai tace “wajen Ya Samira na ara bayan nabiyata da kudin asusu na” Baba yace “saime yafaru”? Cikin kuka sosai tace “ina zaune kan masai nasa earpiece a kunne kawai naga mutum yashigo yana kokarin cire wando” dukansu sukace “Meya miki kike ihu” jikinta har bari yake tana haki tace “wlh babu abinda yamin tsoro naji nadauka aljani ne saisa nadinga ihu na manne jikin kofa shine yamin ihu yace nafita nace ban iya bude kofaba shine yace na matsa yabudemin na fice yay min ball da jaka da wayan Ya Samira harta fashe na kawasa na tafi shikenan” kaman jira Mama take tace “wlh wlh karya kike ke yanzu ki kalli tsabaragen idanun Babanki da Baffan ki kina karya, kifadi gaskiya tun yaushe kika fara iskanci eh? Daman naga gabobin jikinki sai kara habbaka suke waya koyamiki? Wayake matseki? A ina kika sanshi dahar kuka hadu abayi yaushe kika dawo Yar iska mayyan maza Lujain”? Wani kalan fashewa da kuka sosai Lujain tayi tama kasa magana sabida yanda kukan yafi karfinta jin maganganun Mama, tashi Gwaggo tayi tana kakkabe jikinta takalli Baba tace “ku kaini kampanin yanzun nan” kallonta sukayi duka cikeda bala’i tace “ku kaini kampanin nan Kona tare abin hawa nakai kaina, koya mata wani abu kobai mataba bai isa tasanadin shi a batamin sunan diya ba a yanar gizo duniya tagama ganinta, wlh wlh yau sai anyita an kare” Baffa Abdulhadi yakalli Baba yace “Baba dole dama muje muganshi idan ma za’a kai kara hukuma ne asan nayi kumuje” Ahankali Baba yabude motarshi suna suka bude tasu aka shiga har akakai company nan kuka Lujain takeyi sai yanzu tagane abinda yasa su Princess suka kirata har karuwa dudda bata kallo video ba suna kaiwa company reporters dasuka gani agaban kampanin sunfi hamsin saukowa akayi Gwaggo takama hannunta suka wuce ciki ganin ana musu hoto mayafin jikinta tayaye tayafama Lujain dake kuka tarike hannunta sukai wajen shiga taresu security yayi Gwaggo da idanunta sukai jajir tace “na rantse maka da ubangiji zan tube nai dambe dakai awajen nan kace bazamu shiga ba, dan ubanka Mudi da Uwarka Safara’u idan akai kokarin batama jikanka suna bazakayi abinda yafi haka ba budemin kofa kona fasa” girgiza mata kai yayi yace “Mama Oga yace ba shiga ba fita bakiga yan jarida sun cika nan ba” cikin ihu Gwaggo tace “yo ina ruwana shi yasan Meyayi ai” jin yanda Gwaggo ke ihu Hamza da idanunshi sukai jajir yazo wajen daga ciki ganin student din makarantan nan da aka lullube da mayafi tana kuka sosai from yanda jikinta ke bari ga wayanda ke tareda ita dazai iya cewa iyayenta ne yasa ahankali yace “kushigo” bude musu kofa akayi Gwaggo taja hannun Lujain suka shiga ciki, waje yanuna musu awajen yace “ku zauna bari naje na sanar” cikin ihu Gwaggo da idanubta sun juya tace “nabaka minti biyu” stairs yayi karo yaci da Ibro da shima idanunshi sunyi jajir yana kallon su Gwaggo da yarinyan dake sanye da uniform da aka lullube da gyale ahankali Hamza yace “I think is the girls family ka kira Uncle Musty” gyadamai kai yayi yace “yama iso he’s trying to come inside” daidai lokacin wayanshi yahau ringing dasauri Hamza yace “Hajiya ko” gyadamai kai yayi ahankali, hawaye ne yakawo idanun Hamza dan he’s a very soft person yace “kana tunanin tasani” gyadamai kai yayi yace “kaima kasan that’s the only answer to yanda taketa kiranmu tun dazu clean those tears if our workers saw that kanason suyi tunanin Ya Imran zai iya aikata abin ne” girgixamai kai tayi daidai lokacin Musty na sanye da kayan sojoji da Haruna dakuma wani babban abokinsu police man su uku suka taho ganinsu yasa Musty yace “calm down you all Ya Imran din”? Ahankali Ibro yace “yana office working as if nothing is happening amman nasan deep down he’s hurting bama wanan ba Uncle Musty I believe the girl’s parent are here gasuchan” yanunasu ahankali Uncle yace “Innalillahi wa innailaihi raji’un! Allahumma ajirni fi musibati” yakalli hannu da police man yace “kuje ku kutaho dasu lemme see him” yana maganan yawuce sama su Hamza suka bishi ahankali yabude kofan office din Abee, kallo daya Abee yamai yacigaba da aikin dayakeyi bazaka iya gane takamaiman reaction dake kan fuskanshi ba karasawa gaban table din Musty yayi ahankali yace “the girl’s parents are here” chack ya tsayar da typing din dayakeyi batare daya kalli Musty ba, anatse Musty yace “nace su Harun su taho dasu nan we need to speak to them and show them, but maisa baka fadamin komi ba eh Imran” dago idanunshi Abee yayi yama Musty wani kallo yace “me kake so nagaya maka takamaimai nace maka wani anonymous number sent me a text demanding 100M and this company’s document koyay releasing video tarayyana da wata da I know nothing about!”?

Knocking kofan akayi kallon Abee Mustafa yayi yace “gasunan” sanan yajuya yace “bude musu kofa Hamza” juyawa Hamza yayi ahankali yabude kofan Haruna da Police nan mai suna Abdul ne suka shigo sai Gwaggo data rike hannun Lujain gam dake lullube suka shigo tana hura hanci sai Baba dasu Baffa da Yayan Lujain sai Mama wuri harun yanuna musu kan dogon setin kujerun office din zazzamansukayi Gwaggo ta zaunar da Lujain da sheshekan kukanta kawai ketashi acikin office din itakuma Gwaggo tabi kowa na office din da kallo tace “nifa ba zama takawoni ba waye mutum dayaja sunan diyata yabaci aduniya ina mai kampanin?” Ahankali Abee da kanshi ke kasa yadago kanshi gently yazubama Gwaggo idanunshi da hakanan kawai taji magana ya makale abakinta.
💫 SAKON SO 💫

Leave a Comment





No one has commented yet. Be the first!
Leave a Reply