Hausa Novels Saran Boye Hausa Novel

Saran Boye 28


Saran Boye 28
Viral

No. 28

…………Sake buɗe idanun yay ya saukesu bisa giza-gizai dake yawo cikin hasken sararin samaniya na yanayin asubahi. Karan farko a rayuwarsa da zuciyarsa ta tafi wajen tunanin da girmama UBANGIJI da ya halicci sammai, gata dai babu icce ko ɗaya daga kowacce kusurwa ta duniya da zakai zaton ta riƙeta. Sannan babu wata sarƙa ko ƙarfe da suma suke amsa sunan ginshiƙi a gareta. Da rana hasken *_Rana_* ya mamayeta. Da dare hasken *_Wata_* ya ƙawata ta da adon taurari. da *_Damuna_* na _Giza-gizai_. Lokacin asubahi takan canja kala zuwa sky blue da wasu ado masu ban mamaki da al’ajabi. Hakama da yammaci lokacin faɗuwar rana takan ƙawatu da kalar sky blue da na yanayin faɗuwar rana. Duk wannan hikima da rahamar akan azurtamu da sune babu ko naira ɗaya. Babu kuɗin haraji babu na ƙarshen wata. To miyasa wanda ya azurtamu da ita bai taɓa jiran mu biyasa da ko taro ba?  ‘saboda shi ɗin *_(SARKI NE GAGARA MISALI DA BAUTA KAWAI AKE KAƊAICE SA)’_*
Wani yanki na zuciyarsa ya bashi wannan amsar.
Samun kansa yay da sake lumshe idanu ya sauke wasu tagwayen ajiyar zuciya saboda wata kalma data faɗo cikin kunnensa daga massallacin da aka kira salla dan sun saka tafsir ne.. (Kana son sanin ni’imar dake cikin addinin musulinci?). Furicin ya fito daga bakin Sheikh Sooraj Hashim jibiya (Baba malam) dan sun saka tafsir ɗin nasa ne.
‘Tabbas ina son sanin ni’imar dake cikin addinin musulinci?’. Ya amsa tamkar shi ɗin akeyima tambayar kai tsaye. yana mai cigaba da kallon yanda wata keyin ƙasa cikin giza-gizai alamar lokacin faɗuwarsa yayi, zai bama rana guri itama tazo ta cika umarnin ALLAH (S.W.A) akan aikinta.
Tabbas wannan tambaya ta tsayama Yoohan a zuciya. Dan da ita ya ƙarasa sauran daren daya rage masa. Akan kunnensa har aka kira assalatu akai salloli a massalatai. Sai da gari yay haske sosai sannan ya iya barin jikin Window ɗin zuwa toilet.
Ji yake a ransa bazai taɓa samun nutsuwa ba sai ya dangane da gidan baba malam a safiyar nan. Dan tabbas yana buƙatar sanin (Hanyar fahimtar ni’imomin dake cikin addinin musulinci? A yau).

A gaggauce ya gudanar da komai. Kamar ko yaushe yay shirinsa cikin ƙananun kaya. Blue jeans da farar shirt mai gajeren hannu. Sai ya ɗora suit jacket fara tas itama. Yau dai bai saka necktie ba, maɓallin shirt ɗinma ba duka aka rufe ba. Cikin ƙamshinsa ya baro cikin hotel ɗin batare daya nema inda su Solomon suke ba.
Safiya ce sosai a garin, hakan yasa da ƙyar ya samu keke napep, shima da mutum ɗaya a ciki. Bai damu ba, duk da kuwa wannan shine karan farko a tarihin rayuwarsa da zai shiga napep ɗin. Lokacin da mai napep ya tambayesa ina zasa? Da ƙyar ya iya haɗa hausan ya bashi amsa da sunan baba malam kawai. Dan dama bawai ya iya hausan bane yana dai jin abubuwa sosai saboda mu’amula da mutane marasa lafiya akan aikinsa. Sai dai bai iya maidawa, bayan gaisuwa sai abubuwan da baza’a rasaba suma ɗai-ɗai ne.
Sai da aka fara ajiye wanda ya tarar a ciki kafin shi a kaisa. Kusan dubu uku ya miƙama mai napep ɗin. Da mamaki shiko yake kallonsa, yama rasa mizai ce masa dan ya fahimci hausa ba isarsa tayi ba. Sake miƙo masan da yayne ya saka mai napep ƙoƙarin haɗa ɗan turancinsa ya sanar masa naira ɗari da hamsin ne kuɗinsa. Duk da dai turancin bai haɗu da ƙyau ba Yoohan ɗin ya fahimci mi ya faɗa. Dan haka ya ajiye masa kuɗin a jiki yana faɗin, “Na baka ne duka”. Yanda yay maganar da hausa abin dariya, harma mai napep ya kasa haƙuri sai da ya dara.
Yoohan baibi takansa ba ya nufi ƙofar gate ɗin su baba malam kansa tsaye, kai kace gidansa yazo.
Sau uku yay Knocking sannan maigadi ya buɗe ƙaramar ƙofar ya leƙo yana tambayar “Wai wanene haka da farar safiyar nan?” dan yasan su Baba malam ta ƙaramin gate sukaje massallaci yau.
Bai gane Yoohan ba. Dan duk zuwan da yay har sau biyu bashi kaɗai ya shiga ba sai da jagorancin masu gidan. Sai da ya gama ƙare masa kallo sama da ƙasa kafin yace, “Samari lafiya kuwa? Mikake nema ko buƙata anan?”.
Sam Yoohan bai fahimta ba, bayan kalmar (lafiya da wasu ɗai-ɗai) babu abinda ya gane a zancen maigadi. Sai yay shiru yana kallonsa cike da nazarin miya kamata ya ce da shi. Maigadi da haushi ya kama ya sake maimaita masa tambayar?. Nan ɗinma dai ba fahimtar yayi ba. Sai ma ya jefa masa tambaya da turanci shima.
“To bakajin hausa kenan?”. Maigadi ya faɗa a hankali. Sai kuma ya kalli Yoohan yay masa alama da hannu (wai yana zuwa). Kafin Yoohan ɗin yace wani abu maigadi ya koma ciki. Saurin yunƙurowa Yoohan ɗin yayi zai tsaidashi sai dai tuni ya rufe ƙofar.
Cike da damuwa ya dafe kansa. Sai kuma ya juya yana kallon titin anguwar. babu mutane sosai, sai tsilli-tsilli dake fitowa cikin massallacin. Sai kuma sautin karatun yara da shima alama ta nuna daga harabar massallacin ne.
Nufar gate ɗin massallacin yayi, kasancewar shi a buɗe yake sai ya samu damar shiga kansa tsaye. Sai dai bai kai tsakkiyaba wani cikin almajiran malam ya tsaidashi da sauri, dan kallo ɗaya zai tabbatar maka Yoohan ɗin ba musulmi bane.
Anyi sa’a almajirin malam najin turanci, sannan kuma duk zuwan da Yoohan yayi gidan sau biyu ya gansa. Ba ƙaramin daɗine ya kama Yoohan ba jin cewar almajirin malam najin yaren da shima yake ji. Cikin sauƙi suka gaisa ya sanarmasa wajen malam yazo. Kuma yana cike da ƙaguwar san ganinsa domin dalilin babban uziri.
Duk da almajirin malam yayi mamaki hakan bai hanashi yarda zaima Yoohan ɗin iso ba. Dan haka ya nuna masa wani ɗan dakali alamar ya zauna ya jurasa. Shi kuma ya juya cikin massallacin inda yasan malam na zaune yana karatu da azkar kafin ya fara karatu ga magidantan anguwar dakan ɗauki karatun safe da baya wuce zaman awa guda.

Yoohan bai zauna ba. Sai ma faman bin massallacin yake da kallo. A ransa yana sake jinjina ƙoƙarin da su baba malam sukai wajen ginashi. Dan ƙaton gaske ne, kuma ya ginu da gini mai ƙyau. Gashi an shafesa da farin fenti yanata ɗaukar ido tamkar ba’a shiga cikinsa, sai shukoki da suka sake ƙawata shi suma. Ko ina kuma a tsaftace yake. Daga wajen da yake tsaye yana shaƙo daddaɗan ƙamshin dake fitowa daga massallacin wanda kullum safiya da maraice Nu’aymah ke zuwa ta sharesa ta saka turaren wuta da kalolin Air Fresheners masu daɗin ƙamshi……….
Kukan wani yaro ne ya katse masa tunanin nasa. Ya ɗan juya inda yake jiyo kukan. Hakan yayi dai-dai da fitowarta daga cikin ajin da take koyarwa riƙe da bulalar dorina. Sanye take da dogon hijjabi mai hannu fari tas dan har yana jan ƙasa. Hannunta na dama riƙe da Al-qur’ani, na haggu kuma bulala. Yanda take jijjiga bulalan tana magana da nuna yaron ne ya sakashi shagala da kallonta. A ransa ya raya, ‘Ashe kowa ma masifa take masa?’. Jiba dai yanda takema yaro ƙarami duk da kuwa bayajin mi take faɗa. Amma yanayinta ya nuna faɗa takeyi dan tama saka yaron kneeling ne a ƙofar ajin………
“Yahya! kai ne da safen nan?”.
Maganar baba malam ta katsesa daga kallon Nu’aymah daya shagala yi. Numfashi ya sauke tare da juyowa ga baba malam ɗin. Baba malam daya juya yana kallon abinda Yoohan ɗin ya shagala kallo shima ya ɗauke kansa ya maido garesa. Sake mai-maita masa tambayar yayi a karo na biyu.
Yoohan da ya sunkuyar da kai ƙasa yace, “Uncle, inason sanin minene ni’imomin dake a cikin addininku na musulinci?!”.
Ba baba malam da yayma tambayarba, hatta Abban su Abdallah dake fitowa daga massallacin sai da ya taka wani uban birki.
Baba malam da jikinsa ya hau tsuma yace, “Yoohan sake maimaitawa naji”.
Babu musu Yoohan ya kuma faɗin,
“Ina son sanin ni’imar dake cikin addinin musulinci?!”.

الْحَمْدُ للهِ الَّذِي بِنِعْمَتِهِ تَتِمُّ الصَّالِحَاتِ .
Alhamdu lillahil-lazee bini’imatihi tatimmus-salihat.
Godiya ta tabbata ga ALLAH wanda saboda ni’imarsa ce kyawawan ayyuka suke cika.
اَلْحَمْدُ ِللهِ عَلَى كُلِّ حَالٍ.
Alhamdu lillahi ala kulli halin
Godiya ta tabbata ga ALLAH a cikin kowane hali.

Sai ya durƙusa a ƙasa yay sujida hawaye na sauka masa a fuska.
Yoohan dake binsa da kallo yay saurin duƙawa shima yana zaro manyan idanunsa a waje. durƙushewa yay gwiwa bibbiyu yana kallon malam harya ɗago daga sujidar da yay.
Fuskarsa ɗauke da murmushi ya kama Yoohan suka miƙe tare, sai kawai ya jawosa jikinsa ya rungume.
Duk da ba yaune karan farko da aka fara yima Yoohan irin wannan rungumar ba sai yaji ta yau ɗin kamar daban ce a rayuwarsa. Kamar ba irin wadda Papa da sauran mutane ke masa bace. Kamar girman ta yau ɗin na musamman ne.
Baba malam ya ɗagosa da sauri tare da riƙe hannunsa. Yace, “Lallai yau zaka fara sani da ga rahamar UBANGIJINA, domin kuwa, *HASKE da RAHAMAR UBANGIJIN* al’arshi ta bayyana a zuciyarka da harshenka Yahya!. Sai dai bazaka taɓa fahimtar tarin ni’imomin dake cikin musilinci ba daga wajensa har sai ka shigo cikinsa”.
Yoohan da bai fahimcesa ba yay shiru yana kallonsa ƙasa-ƙasa. Sai kusan seconds goma ya ɗago kaɗan ya kalli baba malam ɗin da ƙyau, sai kuma ya sake maida kansa ƙasa. “Uncle ban gane mikake nufi ba”.
Murmushi baba malam yayi, ya sake gyara tsaiwarsa cikin harshen turancin da suke magana yace, “Ina nufin bazaka taɓa fahimtar ni’imomin dake tattare da wannan addini mai daraja ba har sai ka kasance musulmi Yoohan. Ta wannan hanyar ne kawai zaka ƙwanƙwaɗi madarar ni’imar UBANGIJI fiye da zaton hasashen ka”.
Babu ko tantama Yoohan yace, “Inhar zan sani ɗin ta wannan hanyar zan biya ko nawane na shiga addinin naku dan na sani, dan na tabbatar idan ban sani ɗinba natsuwa zata cigaba da yin nisa da ni har abada”.
“UBANGIJI kai ne gagara misali a tunanin hankali ko hasashen zuciya. Tabbas kai mai ikone ga wanda kaso, a kuma lokacin da kaso. Yahya shiga addinin musilinci ba’a biyan ko sisi. *_ALLAH maɗaukakin sarki ya halicci halitta ne domin su bauta masa, kuma ya sawwake musu abinda zai taimaka
musu na arzikinsa, ALLAH maɗaukakin sarki yana cewa:_*
_“Kuma ban halicci aljan da mutum ba sai domin kawai su bauta mini. Bana neman wani arziki daga gare su kuma bana bukatar da su ciyar da ni. Lalle ALLAH shi ne kaɗai mai azurtawa kuma ma’abocin karfi sosai”._ Suratuz Zariyat, aya ta:56-58.
*_Mutum a halittar da ALLAH ya yi masa zai bautawa ALLAH ne shi kaɗai inda za’a bar shi, ya zama mai son ALLAH ya na bauta masa ba ya yi ma sa shirka, sadai abinda ya
ɓata wannan (dabi’ar) kuma yake karkatar da ita shi ne abin sheɗanun aljanu da na mutane su ke ƙawata mata na abinda sashin su yake yi wa sashi wahayi na ƙawatacciyar Magana kawai don ruɗi, shirka wata aba ce da ta zo daga baya kuma ta kutsa kai ga halittar da ALLAH
ya yi wa mutum, ALLAH maɗaukakin sarki yana cewa:_*
_“To, ka tsayar da fuskarka ga wannan addini kana mai kaucewa shirka, halittar ALLAH wacce ya halicci mutane a kan ta, babu mai canza halittar ALLAH”._ Suratur Rum, aya ta: 30.
*Kuma Ma’aikin ALLAH (S.W.A) ya ce: “Dukkan abin haihuwa ana haihuwarsa ne akan musulunci, to iyayan shi ne su ke yahudantar da shi, ko su Nasarantar da shi (kiristan da shi) ko su majusantar da shi”. Bukhari da Muslim ne su ka ruwaito.*
Dan haka Yahya UBANGIJI baya buƙatar ko sisi da ga gareka face amsa kalmar *_La’ilaha illallah……._*”.
Sosai abin ya bama Yoohan mamaki da wannan bayani na baba malam. dan haka ya gyaɗa kansa yana mai gyara tsaywarsa da faɗin, “Na shirya amsar wannan kalma Uncle”.
Murmushi sosai ya sake faɗaɗa a fuskar baba malam, batare da ya sake cewa komai ba ya kama hannun Yoohan sukabi ta ƙaramar ƙofa zuwa cikin gida. Abban su Abdallah na biye da su zuciyarsa fal tunanin inda ya taɓa sanin mai kama da Yoohan ɗin a wasu shekarun baya..
Sashen mahaifinsu kai tsaye suka nufa, ko ina fes yake dan ana gyarawa saboda sukan zauna a ciki musamman randa sukaso nishaɗi. Duk hidimar bikin salla ma jiya a ciki sukayita su huɗun. Sai da duk suka zauna, Yoohan da Abban Abdallah kowa nama ɗan uwansa kallon sani baba malam ya katsesu da faɗin.
*_“Shaidawa Babu Abin Bautawa Da Gaskiya Sai ALLAH, Kuma Muhammadu MANZON ALLAH ne”_*.
_“Waannan kalmomin shahada guda biyu, sune ƙofar shiga musulunci, sune kuma rukuninsa mafi girma, kuma ba a yin hukunci da musulusncin mutum, sai da furuci da su, da kuma aiki da abin da suka ƙunsa, da wannan ne kuma kafiri yake zama musulmi._
1-Ma’anar kalmar shahada: Ma’anar shaidawa da cewa babu abin bauta da gaskiya sai ALLAH, shi ne yin furuci da ita tare da sanin ma’anarta, da kuma yin aiki da abin da ta ƙunsa, zahiri da baɗini, malamai sun haɗu akan cewa furuci da kalmar shahada, ba tare da sanin ma’anarta ko yin aiki da abin da ta ƙunsa ba, ba shi da amfani, kai sai dai ma ta zama hujja a kansa, kuma ma’anar (La Ilaha Illallah) shi ne babu abin bautawa da gaskiya sai ALLAH shi kaɗai matsarkaki maɗaukaki.
_Rukunan wannan kalmar (shahada) sune: (korewa da tabbatarwa), wato kore haƙƙin bauta daga wanin ALLAH, kuma tabbatar da shi ga ALLAH shi kaɗai ba shi da abokin tarayya. Haka kuma wannan kalmar ta ƙunshi kafircewa ɗagutu (shi ne dukkannin abin da ake bauta masa wanda ba ALLAH Maɗaukaki ba, ko da kuwa ya kasance mutum ne (tare da yardarsa da bautar da ake masa), ko dutse, ko bishiya, ko son zuciya, ko sha’awa), da nuna masa ƙiyayya da yin kuɓuta daga gare shi._
*_Wanda ya faɗi wannan kalmar (shahada da bakinsa) amma bai kafircewa abubuwan da ake bauta
musu wanin ALLAH ba (a aikace), to tamkar bai faɗeta ba. ALLAH Maɗaukaki ya ce: “Kuma abin bautarku abin bauta ne guda ɗaya.
Babu wani abin bauta wa da gaskiya sai Shi. Mai rahama Mai jin ƙai”.(Baƙara: 163)._*
*_Kuma Maɗaukaki ya ce: “Babu tilastawa game da (shiga) addinin
(musulunci), haƙiƙa shiriya ta bayyana daga ɓata, saboda haka wanda ya kafirce wa ɗagutu kuma ya yi imani da ALLAH, to haƙiƙa ya riƙi igiya amintacciya, (wadda) ba ta yankewa. ALLAH kuwa Mai ji ne, Masanine”._* (Baƙara: 256)
_Kuma kalmar (Ilah) tana nufin abin bautawa da gaskiya, duk wanda ya ƙudurci cewa abin da ake nufi
da kalmar (Ilah) shi ne: Mai halitta, Mai arzutawa, ko wanda yake da ikon ƙirƙira, kuma ya ƙudurci cewa yin
imani da wannan kawai zai wadatar, ba tare da kaɗaita ALLAH da ibada ba, to haƙika faɗin kalmar (La Ilaha
Illallahu) ba za ta amfane shi ba, a nan duniya wajen shiga Musulunci, kuma a Lahira ba zata kubutar da shi ba daga azaba madawwamiya._
ALLAH Maɗaukaki ya ce: “Ka ce (da su): “Wane ne yake arzuta ku daga sama da ƙasa? ko kuma wane ne yake mallakar ji da gani?, kuma wane ne yake fitar da mai rai daga matacce, ya kuma fitar da matacce daga mai rai? Wanene kuma yake tsara al’amura?” To za su ce: “ALLAH ne”. To ka ce (da su): yanzu ba za ku ji tsoronsa ba?”
(Yunus: 31).
*_ALLAH Maɗaukaki ya ce: “Ko wane ne ya halicci sammai da ƙassai, ya kuma saukar muku da ruwa daga sama, sannan (da wannan ruwan) muka tsirar da (shukokin) gonaki
masu ƙayatarwa, ba kuwa za ku iya tsirar da bishiyoyinsu ba?, shin akwai wani abin bautawa tare da ALLAH, A’a, su dai mutane ne da suke kauce wa (gaskiya)”. (Naml: 60)._*
Kuma ALLAH Maɗaukaki ya ce: “Kuma lallai idan ka tambayesu, “Wanene ya halicce su?, Lallai za su ce: “ALLAH ne” To, yaya ake juyar da su (daga bauta wa ALLAH)?” (Zukhruf: 87).

*_“Ma’anar Shaidawa Lallai MUHAMMADU MANZON ALLAH ne:_*
_Ma’anar shaidawa lallai (Annabi) Muhammadu
MANZON ALLAH ne shi ne a yi masa biyayya cikin abin da ya umarta, da gaskatashi a kan abin da ya ba da
labari, da nisantar abin da ya hana kuma ya yi tsawa a kansa, kuma ba za a bautawa ALLAH ba sai da abin da ya
shar’anta._
*_Tabbatar Da Shaidawa Lallai MUHAMMADU MANZON ALLAH ne:_*
_ MANZON ALLAH ne: Shaidawa lallai (Annabi) Muhammdu Manzon
ALLAH ne tana tabbata ne da yin imani da cikakken yaƙinin cewa lallai (Annabi) Muhammdu tsira da amincin ALLAH su tabbata a gare shi bawan ALLAH ne, kuma Manzonsa ne ya aiko shi zuwa ga Aljanu da mutane gaba ɗayansu, kuma lallai shi ne cikamakin Annabawa da Manzonni, kuma shi Annabi tsira da amincin ALLAH su tabbata a gare shi bawa ne makusanci a gurin ALLAH ba shi da komai daga siffofin ALLAH, kuma (wannan shaidar tana tabbata ne) da yi masa biyayya da girmama umarninsa da haninsa, da lazimtar
sunnarsa a baki, a aikace, kuma a ƙudurce._
*_ALLAH ya ce: “Ka ce: ya ku mutane lallai ni MANZON ALLAH ne
zuwa gare ku gaba ɗaya” (A’araf: 158). _*
_Kuma ya ce: “Ba mu kuma aiko ka ba face zuwa ga mutane baki ɗaya, kana mai gargaɗi da bushara” (Saba’a: 28)._
_Kuma ya ce: “(Annabi) Muhammadu bai kasance uban ɗaya
daga mazajenku ba, sai dai (shi) Manzon ALLAH ne kuma cikamakin Annabawa” (Ahzab: 40)._
_Kuma ya ce: “Ka ce tsarki ya tabbata ga Ua
UBANGIJINA, ni ba
kowa ba ne face mutum kuma Manzo” (Isra’i : 93)._
Wannan (tabbatar da shaidawa Annabi Muhammadu Manzon ALLAH) ya ƙunshi al’amura kamar
haka:
Na farko: yarda da Manzoncinsa da ƙudurceshi a ɓoye cikin zuci.
Na biyu: yin furuci da haka da harshe a bayyane.
Na uku: koyi da shi da yin aiki da abin da ya zo da shi na gaskiya, da barin abin da ya hana na ƙarya.
*_ALLAH Maɗaukaki ya ce: “Sai ku yi imani da ALLAH da Manzonsa, Annabi Ummiyyi¹, wanda yake imani da ALLAH da kalmominsa, kuma ku bi shi don ku shiriya” (A’araf:
158)._*
Na huɗu: gaskatashi a kan dukkan abin da ya ba da labarinsa.
Na biyar: Mutum ya so shi sama da son kansa da dukiyarsa da ɗansa da mahaifinsa da mutane baki ɗaya; domin shi MANZON ALLAH ne, kuma haƙiƙa sonsa yana daga cikin son ALLAH, da so saboda ALLAH Haƙiƙanin son MANZON ALLAH shi ne yi masa biyayya wajen bin umarninsa da nisantar haninsa da
taimakonsa da jibintarsa.
*_ALLAH ya ce: “Ka ce: idan kun kasance kuna son ALLAH, to ku bi
ni, sai ALLAH ya so ku, ya kuma gafarta muku” (Ali Imran: 31)._*
Kuma ANNABI tsira da amincin ALLAH su tabbata a gare shi ya ce: “Ɗayanku ba ya zama mumini har sai ya soni fiye da mahaifinsa da ɗansa da mutane gaba ɗaya” Bukhari da Muslim ne suka ruwaito shi daga hadisin Anas ALLAH ya yarda da shi.
*Kuma Allah Maɗaukaki ya ce: “Saboda haka waɗanda suka yi imani da shi, suka kuma girmama shi, suka kuma taimake shi, suka kuma
bi hasken da aka saukar a tare da shi, to waɗannan su ne marabauta” (A’araf: 157).*
Na shida: Ƙudurce cewa sunnarsa asali ce ga shari’ar musulunci, kuma ita sunnar kamar Alƙur’ni mai girma take (wajen dogoro da aiki da ita), saboda haka ba a saɓa mata domin hankali ya ci karo da ita.
Na bakwai: yin aiki da sunnarsa da gabatar da maganarsa a kan maganar kowa, da miƙa wuya zuwa
gare shi, da yin hukunci da shari’arsa da yarda da ita.
*_ALLAH Maɗaukaki ya ce: “Na rantse da girman UBANGIJINKA ba za su yi imani ba, har sai sun sanyaka mai hukunci game da abin da ya faru a tsakaninsu, sannan kuma ba su sami
wata ƙunci ba a zukatansu game da abin da ka hukunta, su kuma miƙa wuya gaba ɗaya” (Nisa’: 65)._*……………✍

ZAFAFA BIYAR 2021

Hafsat miss xoxo🥰
KIBIYAR AJALI……!
(Sulke baya tareta saita gitta).😋🤗

Mamu gee🥰
MIN ƘALB!!😋🤗

Hafsat rano🥰
ABINDA KE CIKIN ZUCIYA…!!😋🤗

Safiyya huguma🥰 SIRAƊIN RAYUWA😋🤗

Bilyn Abdull🥰
SARAN ƁOYE🤗😋

Duka akan farashi mai rahusar gaske.

Kamar haka👇🏻💃🏻

Ɗaya___300
Biyu____400
Uku_____450
Huɗu____500
Biyar_____700

Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇

ACCOUNT NO 0812652655
ACCOUNT NAME- HAFSAT LAWAN GAMBO
BANK NAME: ACCESS BANK.

saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇

0903 234 5899

IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇

09033181070

💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻
TEAM—-ZAFAFA BIYAR🔥😘🥰😍

ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻.
[5/18, 6:00 PM] +234 808 711 8630: *_LITTAFIN nan na kuɗi ne. Dan girman ALLAH ki daure ki biya kafin ki karanta, idan kuma bazaki iya biya ba ki haƙura domin ALLAH karki karanta. Idan kuma kin saya dan girman ALLAH karki yaɗa mana🙏🏻_*.

 

Leave a Comment





No one has commented yet. Be the first!
Leave a Reply