Hausa Novels Saran Boye Hausa Novel

Saran Boye 7


Saran Boye 7
Viral

No. 7

…………….Sosai gazawar Umm take ƙoƙarin bayyana ga kowa. Dan gaba ɗaya yinin yau da Nu’aymah ta yisa a ranta. Tun tana kukan zuci kamar yanda ta saba har hawaye suka kai ga fara sakko mata daga idanu.
Wajen misalin biyu da rabi na rana Baba malam ya shigo gidan. Kamar yanda al’adarsa take inhar ya dawo daga wajen aiki sai ya fara zuwa sashen Hajjo yaga lafiyarta. yauma haka ne. Zaune ya isketa a falo Imran na tausa masa ƙafa yana kumbura baki dan ta sakashine dole.
Murmushi Baba malam yay da zama a ƙasa gefenta kaɗan da ajiye mata ledan kayan fruits idonsa akan Imran ɗin da shi sam hankalinsa bai kai kansa ba.
“Imran ya naga fuskar a kumbure? Ko dai aikin innah ne ba’a son yi?”.
Kallonsa Imran yay da sauri, sai kuma ya saki ƙafar Hajjo ya nufi baba malam ɗin yana sake tunzura baki gaba. “Baba sannu da dawowa”. Kafin Baba malam ya bashi amsa Hajjo ta katsesa. “Dan gidanku dawo ka cigaba, inba hakaba kasan ALLAH nasan ta inda zan rama mai ƙwalelen ƙeya kawai”.
Dariya Baba malam yayi yana kallon yanda Imran ɗin ya cika yay fam, sai kuma ya kalli Hajjo da itama ta kumbura farar fuskarta da duk tai tamojin tsufa tana zubama Imran ɗin harara……
“Ni wlhy na gaji Hajjo, kumafa Momy jirana take zan mata aika”.
“Oh! Uwarka ta fini kenan?..”
Baba malam yay saurin haɗiye dariyarsa da matsawa kusa da ita gab ya kama ƙafar tata ya aza saman ƙaramin filon kujera. “Kinga Inna manta da shi kinji, idan shima yana tsoron ɓatama mamarsa nima ai gani tare dake ko?”.
Murmushi tayi kamar ba itace da fuska a kumbure ba. Sai kuma ta watsama Imran ɗin harara tana faɗin, “Tashi ka fitarmin a falo to kirikun banza, indai nice ai inada ranata yaro”.
Tashi Imran yay da sauri dan ganin Hajjo ta kwakuso filon kujera da alama dukansa zatayi. Sai da yaje bakin ƙofa sannan ya juyo. “Ai dai gobe idan ALLAH ya kaimu zamuyi komawarmu Abuja…….”
Kafin ya rufe baki ta tilla masa filon, kwasa yay da gudu ya fice yana ƙyalƙyala mata dariya.
“Wlhy Ɗan malam ƴaƴanku sun fetsare musamman ma ƙarshe-ƙarshen nan. Kaga akace maka Imran da Muhammadu da Jafar sunfi kowa rainanima a gidannan”. Hajjo ta faɗa a ƙufule.
Cike da girmamawa da lallashi baba malam yace, “To kiyi haƙuri inna zan musu faɗa kinji, yanzu dai ƙafar ciwo take miki ne?”.
“Kaɗan take ciwon dai, na neman man zafin daka siyomin shekaranjiya na rasa inda yake, na tabbata cikin ƴaƴanku wani ya ɗaukesa. Ƙilama Zainabu c…….” sai kuma tai shiru ta kasa ƙarasawa saboda tunawa da tai Nu’aymah ma bata gidan. To ita kaɗaice ke mata yanda ta gadama a cikin jikokinta a zauna lafiya a gidan. Dan suna mugun ɗasawa da Nu’aymah saboda duk aikin da ta sakata yimatashi take. Hatta da wanki Nu’aymah ce kema Hajjo. Hakama gyaran sashenta. Sai ko Adawiya itama sunaɗan shiri, amma ƙa’ida kullum sai sunyi faɗa.
Ɗan murmushi baba malam yayi mai ciwo, dan shima a kullum ɗiyar tasa tana a ransa. Ya sauke ajiyar zuciya da faɗin, “Karki damu innah insha ALLAH zansaka Abubakar ya saya miki idan zai baro company. Sannan zanma Doctor Kabir magana yazo ya duba ƙafar, idan kuma asibitin zamu koma to”.
Jikinta a sanyaye ta ɗaga masa kanta, harya miƙe bata iya sake cemasa komaiba. Sai da yaje gab da fita sannan ta kira sunansa. “Ɗan malam!”. Juyowa yay da sauri yana ƙoƙarin haɗiye abinda ya tokare masa maƙoshi da amsawa da “Na’am Innah”.
“Har yanzu babu labarin Zainabu dai ko?”.
Murmushin yaƙe yay mata wanda yafi kuka ciwo, ya ɗan girgiza mata kansa da faɗin, “Innah tasan inda taje ta ɓoye kanta ai. Randa ta buƙaci ganinmu da kanta zata nememu, ki kwantar da hankalinki wannan yabar damunki”.
Bata iya cewa dashi komaiba yanzuma. Dan damuwa ƙarara ta hango a saman fuskarsa da cikin idanunsa. Amma dan ƙarfin hali sai yay mata murmushi sannan ya juya ya fita.

Tamkar wanda aka zarema lakar jiki haka ya isa sashensa. Da tsarabar da yayo ta fruits ya fara cin karo a falo alamar driver baiga kowaba ya ajiye a nan. Ya ɗanbi ledojin da kallo kafin ya ida shigewa cikin corridor ɗin da ɗakunan barcin su Umm suke. Kansa tsaye ɗakinta dake can ƙarshen dogon corridor ɗin ya nufa, yay sallama kusan uku a ƙofar ɗakin babu amsa, sai kawai ya tura ƙofar ya shiga da sallama.
Tsaye yay cak a ƙofar ɗakin riƙe da handle ɗin kofar yana kafe Umm dake zaune a saman gado, Muh’d na kwance ya aza kansa bisa cinyarta yana barci. Kan yaron take shafawa a hankali, kanta na kallon p.o.p idanunta na tsiyayar da hawaye.
Haɗiye tasa damuwar yay ya ƙarasa cikin ɗakin sosai. Harya zauna a bakin gadon kusa da Umm bata motsaba. Ya ɗaura hannunsa saman nata dake shafa na Muh’d. Nannauyan numfashi ta sauke da ɗago kanta. Kallon ido cikin ido sukaima juna ita da baba malam ɗin. Sai tai azamar saka hannunta na haggu ta share hawayen fuskar tata tana maye gurbinsa da murmushi.
“Sannu da zuwa Abban Nu’aymah. Yaushe ka shigo ban saniba? Gaba ɗaya na gajine shinefa nace bara nazo na………” hannunsa yay saurin ɗorawa akan bakinta alamar tayi shiru. Yasan ba wani abune ya saka wannan kame-kamenba sai dogon gargaɗin daya gindaya mata akan karta sake masa maganar Nu’aymah koda da wasa ne. Umm macece ita mai biyyaya da gudun ɓacin ran mijinta, duk abinda ya nuna bai masaba ƙoƙarinta shine dainashi tai masa wanda zai sakashi a farin ciki koda ita zai cutar da tata zuciyar kuwa. Wannan yana ɗaya daga cikin abinda ya ƙara mata kima da daraja a gareshi, tare da sake girmama soyayyarta a ranshi.
Miƙewa yay ya ɗauki Muh’d a hankali ya matsar dashi can gefe ya kwantar. Ita dai tana binsa da kallone har ya dawo ya zauna kusa da ita sosai. Kamota yay ya kwantar da kanta a ƙirjinsa. A tare suka sauke nannauyar ajiyar juciya. Hawayen da taketa ƙoƙarin karsu zubo suka ziraro a guje suna sauka bisa jikinsa.
Idanunsa ya lumshe tare da sake kwantar da ita jikin nasa da ƙyau, ya zame ɗan kwalinta yana shafa kanta dake cike da gashi dogo mai yarfin furfura ɗai-ɗai alamar girma ya fara kamata. Sake kwanciya tai sosai da cigaba da hawayenta.
Sunja tsahon lokaci a haka har saida akai kiran sallar la’asar sannan. Itace ta ɗagashi da sauri. Hakan yasa ya farka daga barcin daya figesa shima. Tunda abinnan ya faru bai sake yarda sun kwana ɗaki ɗayaba tun randa ta kwana babu lafiya. Hakan yasa suke tsananin kewar ɗumin junansu. Matsar da fuskarsa yay gab da tata ya sumbaci goshinta da dogon hancinta.
Ɗan murmushi tamasa da sadda kanta a ƙasa na alamar jin kunya. Shima yay murmushin yana sauke ƙafafunsa ƙasa. Batare da yace mata komaiba ya nufi hanyar fita yana faɗin, “Ki tada Muh’d yay alwala mu wuce massallaci”.
“To” ta amsa masa tana binsa da kallo.

__________________________________

Ana shiga sallar la’asar jar motar na shigowa cikin layin. Parking yay a ƙofar ƙaton gate ɗin gidan yana kallon gate ɗin massallaci. Kafin kuma ya maido dubansa kan Nu’aymah dake a gefensa hannu da idanunta da baki a rufe tana gyangyaɗi.
Ɗauke kansa yay ya kashe motar gaba ɗaya. Bai fitaba, saima kwanciya yay jikin kujera ya lumshe idanunsa dake a cikin baƙin glasess ɗinsa.
Kusan mintuna uku da tsayuwarsu Nu’aymah ta farka. Sai dai kasancewar idanunta da bakinta a rufe suke sai bazaka fahimtaba. Addu’a kawai take jerawa a ranta na nema agajin UBANGIJI. Sai da aka fito massallaci mutane suka gama shashsharewa, sai hayaniyar yara ƴan islamiyya dake cikin harabar massallacin. Kusan biyar na yamma Baba malam ya fito daga cikin massallacin shi da wani maƙwafcinsu suna magana. Saurin tashi yay zaune da kallon Nu’aymah, yay azamar saka hannu ya ɗaye mata salataf ɗin da suka rufe mata baki da shi. Ƴar ƙarar azaba ta saki tana faɗin, “Mugu kawai, ALLAH zai sakamin”. Bai kulata ba ya kwance mata idanunta da hannunta suma. Wani irin farin cikine ya saukar mata a rai ganinta a ƙofar gidansu. Tana zumuɗin fita ya dakatar da ita.
“Malam ɗauki akwatinki ki wuce da shi”.
Juyiwa tai da sauri tana kallonsa batare da ta saki handle ɗin ƙofarba. “Bansan kallo, ki ɗau akwatinki nace”.
“Minene abin kallo a jikin naka banda baƙin hali da zalunci. Ni dai nasan banbar gidanmu da akwati ba mizaisa kuma na ɗauka na shiga da shi…”
“K!!!” ya daka mata tsawa a fusace. Hakan ya sakata dakatawa daga ƙoƙarin sake buɗe ƙofar ta juya tana watsa masa harara da manyan fararen idanunta masu yalwar gashi. “Minene namin tsawa malam?”. Maimakon ya bata amsa sai ya ɗaga mata yatsun hanunsa biyu dake a cikin safa yana faɗin, “Kinada zaɓi biyu. Koki ɗauka akwatin nan kokuma wlhy na maidake inda muka fito, kuma wannan tafiyar itace zata zamemiki ta har abada keda gida”.
Kafinma ya rufe baki ta miƙa hannu baya ta sungumi ƙaramin akwatinta ruwan hoda mai ƙyau. Batare data sake jira yace uffan ba ta buɗe murfin motar ta fice abinta.

Sosai gaban baba malam ya faɗi, yabi Nu’aymah dake jan akwati zata shiga gida da kallo harta tura ƙofar ta shiga, kafin ya maido dubansa ga motar data ajiyeta. Akan idonsa mai motar yay reverse yabar anguwar.
Duk yanda yaso danne ransa suci gaba da magana da Alhaji Mani hakan ya gagara. sai kawai yay masa sallama akan yayi haƙuri anjima zasu ƙarasa maganar.
Da mamaki Alhaji Mani yabi baba malam da shi harya shige gida da kallo.. Ya ɗanyi shiru alamar tunani. Ganin bai hasaso komaiba sai kawai ya girgiza kai shima ya juya ya shiga nasa gidan da masallaci ya raba tsakaninsu da nasu Baba malam.

______________________
ZAFAFA BIYAR 2021
_______________________

Wannan littafi SARAN ƁOYE na kuɗine, yana ɗaya daga zafafa biyar, idan kana buƙata kaima waɗanan numbers ɗin magana ka biya kuɗinsa naira 300 kacal dan girman ALLAH. Karka yaɗa dan ALLAH idan ka gani😀🤝🏼.

Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇

ACCOUNT NO 0812652655
ACCOUNT NAME- HAFSAT LAWAN GAMBO
BANK NAME: ACCESS BANK.

saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇

0903 234 5899

IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇

09033181070

__________________
__________________

Nu’aymah na isa tsakiyar gidan ta yadda akwatin ta kwasa da gudu zuwa ciki tana ƙwala kiran sunan Umm da Hajjo, dan gani takema tafiyar ɓata mata lokaci takeyi na isa garesu.
Ba Umm da Hajjo kaɗaiba kowa ma na gidan sai da ya fito, yaran ne kawai da suka wuce islamiyya babu. Samarinma yawancinsu sun dawo daga wajen aiki da makaranta ga waɗanda ke jami’a.
Wani irin tsalle Nu’aymah tai ta ɗane wuyan Umm dake tsaye a ƙofar sashenta tamkar wata gunki. Hakan yayi dai-dai da shigowar Baba malam gidan a matuƙar fusace.
“K!! Nu’aymah! K!! Nu’aymah kina ina?”. Baba malam dake shigowa tun daga gate ya fara kwala ma sunanta kira kamar zai haɗiye harshensa.
Da sauri Nu’aymah ta saki Umm jikinta na wani irin rawa, dan abin yazo mata a yanda batai zatonsa ba. Akwatinta dake yashe a ƙasa ya shura da ƙafa yana faɗin, “Zoki ɗauka ki koma inda kika fito kafin harshena ya furta miki abinda har ki ƙare rayuwarki zai zame miki musiba”.
Idanu sosai Nu’aymah ta zaro waje jikinta na sake ɗaukar tsuma. Muryarta na rawar fitar kuka tace, “Abba……” Katseta yay a tsawace yana nuna mata hanya da yatsansa.
Ba’ita mai laifin kawai ba, kowama yayi tsuru-tsuru a gidan hatta dasu Abba Rudwan sun kasa magana, dan sunsan ran yayan nasu a matuƙar ɓace yake. Hajjo ce kawai zata iya sakashi ko hanashi a irin wannan yanayin. Gashi kuma bata fitoba, ƙila wanka takeyi.
“Ba dake nake magana ba ne?!!”.
Fashewa da kuka Nu’aymah tayi ta durƙushe ƙasa. “Abbah wajen waɗanda suka sacenin kakeson na koma?”. Tsaki yaja mai ƙarfi, dan yama ɗauka maganarta raini da iya shege.
“Lallai Nu’aymah kin girma! Ashe wayonki da iya tsara abubuwa har ya kai haka ƙarfi? Ki sanar mana kinbi saurayi saboda kar a aura miki Abdallah sannan ki dawo mana da wani sabon rainin wayon saceki akayi?. To idan saceki akayi uban wanene ya rubuta saƙwannin da kika barmana? Wanene kuma ya sacekin? Wanda naga ya ajiyeki yanzu shima wanene?. Duk sai ki bamu waɗanan amsoshin muna saurarenki?”.
Kai Nu’aymah ta shiga girgizawa tana hawaye. “Wlhy Abbah bansan komaiba akai. Bansan su wanene ba? Bansan wanene wanda ya ajiyeninba nima? Sannan ban ajiye saƙon komaiba ga kowa wlhy”.
“Nu’aymah!!!”. A tsananin tsawace baba malam ya kira sunanta. Sai da hantar cikin kowa ta kaɗa da tsawarsa. Itama tai baya ƙasa wanwar jikinta na ɓari na tsabagen tsorata. Dan bata taɓa ganin fushin mahaifinta irin hakaba duk da tasan yanada zuciya.
Nufarta yay tamkar wani mayunwacin zaki, sai famar huci yakeyi jikinsa na tsuma.
Da sauri Abban Abdallah da Abba Mustapha suka sha gabansa yana gab da isa ga Nu’aymahn. Kareta sukayi yanda bazai ko iya ganinta ba balle ya taɓata.
Sake ɓaci ransa yay, ya kallesu da jajayen idanunsa da ƙwalla suka taru a ciki. kamar zaiyi magana sai kuma ya fasa, ya juya zai zagayesu ya damƙeta.
Caraf aka riƙe masa hannu. Dan haka ya tsaya cak batare da ya shiryaba. Hajjo data fito yanzun nan saboda tsawarsa da taji ta kalli hannunsa data riƙe da tana sake tamke fuska batare da tayi magana ba.
A take dukkanin jikinsa yay sanyi laƙwas, sai wata irin zufa data shiga tsatstsafo masa a goshi. Sun kai kusan mintuna biyar a haka ana kallon kallo tsakanin duka ƴan gidanma. yayinda Umm tunda Baba malam ya shigo ta sulale ta koma ciki tana hawaye.
Da idanu Hajjo tai masa magana da yaren da tun yana yaro ya haddace sa, kafin ta saki hannunsa a hankali ta nufi Nu’aymah dake durƙushe ƙasa tana kuka har yanzun. su Abbah zagaye da ita suma har yanzun suna bata kariya daga baba malam. Kamata hajjo tai ta miƙar da ita ta rungumeta a jikinta. Nu’aymah ta ƙanƙame Hajjo sosai tana jan numfashi da ƙyar. A hankali kuma sai idanunta suka fara lumshewa, kafin kowa ya farga tama sume.
Hajjo da taji ta mata nauyi tai ƙoƙarin ɗagota amma ta kasa. Gabantane ya faɗi tace, “Kai Mustapha zoku duba yarinyarnan kamarma bata da rai”.
Ai kafinma ta rufe baki sun kama Nu’aymah da hanzari. Yaraf tai baya jikin Abban Adawiya alamar dai da gaske bata numfashin. Sake tashi hankalin kowa yayi, duk sauranma suka matso suna ambaton Innalillahi….
Ɗaukarta Abban su Adawiya yay ya nufi sashen Hajjo sauran biye da shi. Yana kwantar da ita bisa kujera Ahmad na miƙo ruwa daya ciro a fridge. Amsa Abban su Abdallah yay ya zuba a hannu sannan ya shafama Nu’aymah a fuska. Ko motsi bataiba balle ai tunanin farfaɗowar ta. Sake tashi hankalinsu yayi. Ahmad da Malam ƙarami suka durƙusa da saurin kama ƙafafunta suna murzawa, suma su Abba hannayen Nu’aymah suketa faman murzawa. Amma abin tashin hankali ko motsi bataiba har lokacin.
A yanzu kam kowa ya fara tunanin ciwon Nu’aymahr ne ya motsa, dan haka Abba Musbahu da bai jima da shigowa gidanba yay saurin faɗin, “Inaga a kira Doctor ɗinta, kamarfa ciwontane ya motsa”.
Cikin kuka Hajjo tace, “Kirashi Musbahu, dan ALLAH ka kirashi da sauri. Innalillahi……… Zainabu karki mutu ki barmu kinji”. Kukan Hajjo ba ƙaramin sake ɗaga hankalinsu yayiba, matan ma sai faman share hawaye sukeyi.

Duk abinda ke faruwa akan idanun Baba malam ne dake tsaye a jikin daga ƙofar falon Hajjo yana kallonsu. Kallo ɗaya zakai masa ka fahimci yana cikin tsananin tashin hankali. Nu’aymah zuciyarsa ce, yana dannewa ne kawai, amma bazai yuwu ya bari son da yake mata ya hanashi hukuntata akan kuskurenta ba, dan yasan icce tun yana ɗanye ake tanƙwarashi, idan ya bushe karyewa yakeyi.

Sun cigaba da ƙoƙarin ganin ta farfaɗo kafin Doctor ya iso, sai dai fa ko motsi babu wani sashe na jikinta dake nuna alamar zaiyi ma………..✍
Tashin hankali😪, kumuje zuwa.

_____________________
SAHFAT PREORDER!
______________________

Wani kaya sai amale ka ɗauka🤗.

SAHFAT PREORDER maida tsohuwa yarinya.

Kaji masu kawo kayan adon gida dana jiki ƴan gaske.

*_Ina mata masu ƴan bana bakwai? ko uwargidar da ake shirin kawoma ƴar bana bakwai?. Kai hardama matan gayu ƴan ƙwalisa masu son sabunta gida da kayan ado ƴan waje masu sauƙin farashi da nagarta!._*

_To ku garzayo dama ta samu, dan SAHFAT PREORDER sune na ɗaya a wannan fanin. Idan kayan kitchen kikeso masu ƙyau da nagarta a farashi mai sauƙi kuma zaki samu a Sahfat preorder. Idan kayan sakawa kikeso na manyan mata ƴan gayu suma akwaisu babu ƙayarya. Jaka ko takalma na nunawa tsara suma ba’a barsu a baya ba harma da mayafai. Hakama kayan ɗaki basu da tsara_.

Ni shaidace domin dukkan kayana ta hannunsu nake samu nima. Ku garzayo kuma a dama daku dan nasan zakuyi alfahari da hakan insha ALLAHU.

Kiyi magana ta wannan Number 08142957548 insha ALLAH zaki samu ƙarin bayani ƴar uwa.

*_Siyen nagari😇, maida kuɗi gida😉 sai SAHFAT PREORDER🤗🤗😘😍😋_*

_____________________________
ZAFAFA BIYAR 2021
_______________________

Hafsat miss xoxo🥰
KIBIYAR AJALI……!
(Sulke baya tareta saita gitta).😋🤗

Mamu gee🥰
MIN ƘALB!!😋🤗

Hafsat rano🥰
ABINDA KE CIKIN ZUCIYA…!!😋🤗

Safiyya huguma🥰 SIRAƊIN RAYUWA😋🤗

Bilyn Abdull🥰
SARAN ƁOYE🤗😋

Duka akan farashi mai rahusar gaske.

Kamar haka👇🏻💃🏻

Ɗaya___300
Biyu____400
Uku_____450
Huɗu____500
Biyar_____700

Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇

ACCOUNT NO 0812652655
ACCOUNT NAME- HAFSAT LAWAN GAMBO
BANK NAME: ACCESS BANK.

saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇

0903 234 5899

IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇

09033181070

💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻
TEAM—-ZAFAFA BIYAR🔥😘🥰😍

ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻.
[5/28, 3:14 PM] Queen Meenali👑: *_Typing📲_*

Leave a Comment





No one has commented yet. Be the first!
Leave a Reply