Bibiyata Akeyi Hausa Novel Hausa Novels

Bibiyata Akeyi 19


Bibiyata Akeyi 19
Viral

Page 19

*

Duk wani tashin hankali, mai martaba yashigeshi. Jin cewa d`ansa mafi soyuya yananan, rayuwa akwai ko babu.

Ganin mai martaba, cikin wannan yanayi yasa akatashi fada Alokacin.

Dakyar mai martaba, Ya tashi ya shige, sha shinsa.

Kunsan yanda zance baya 6uya, barin ma amasarauta, mai girman gaske irin ta kana.

Har yakai kunnan kilishi, alokacin da’akazo Mata da zancen suna tare da intisar da yayanta guda biyu.

Affan Wanda bazaifi kimanin shekara ashirin da biyar ba. Da halima Wanda tayi aure yaranta biyu. Kanwar Affan ce”

 

Bakaramin tashin hankali suka shiga ba, jin mahaifinsu na wani irin yanayi, wanda gab yake da tashin ciwansa.

Nufan shashinsa sukayi, cikin matsanancin damuwa, basu jira anmusu isoh ba,

“Shiga kawai sukayi”
Nan suka ganshi ya kifa kansa,
Affan ne yanufeshi cikin sauri, yarikoshi,

Abbah meye yafaru???????
Dagowa yayi ya kalleshi,
Muhammadu je kayi mana tanadar mana jirgi zuwa dubai,
Tafiyan Karya wuce nan da awah biyu”
Abba me zamu jeyi dubai??????
Yareemah!!!!! Yareemah!!!!!!! Kawai yake fadi cikin sarkewar harshe.

Abbah”” mai yafaru da yaya yareeman??????

An harbeshi!!!!!
Fadin irin tashin hankalin da suka shiga ma bata bakine.
Dan affan kuka yaringa yi kamar Wata mace.
Intisar da halima kuwa kuka sukeyi kamar Wanda akace yamutu.

Kilishi” ne tayi kafin halin cewa, aibe kamata mutafi mu kadai ba,
Mukira sauran yan uwansa sannan muwuce.

Hakan kuwa akayi cikin Kan kanin lokaci akasanar da sauran ‘yan uwansa. cikin awawin da basu wuce hadu ba duka suka hallara. Fadin irin tashin hankalin da suka shiga ma bata hannu wajan typing ne😭😭,
Sosai suka shiga tashin hankali.
Sai wajan bakwai na dare, kafin jirginsu ya daga. ✈.

================

Anyi iyah bin cike , Dan gwano wayanda suke da hannu awannan aika aikan ankasa, Dan kokadan bbu Wata shaida da zata nuna hakan.

Wannan aikin dole dasa hannun wasu manyan acikinsa, dama daniel yana raye ne to da akwai hanyoyin da zasubi Dan gano wayannan masu laifi.
Amma tun harbin da captain Ahmed ya yi masa, daniel ko shurawa baiyiba ya mutu
Amma a nanan an kara karfafa tsaro da bincike.

Bayan kaman awah biyu da kaishi dakin hutu, wani likita yashiga dan dubashi,
Alokacin kuwa hankalin Ummii yakai kololuwa wajan tashi, dan Har yanzu bawani gamsheshen labari gameda halin da d`anna ta yake ciki.

Likitanne yaje shiga tayi saurin tsareshi, tana tambayarsa yasanar da ita!!! Halin da d`anta yake ciki , Idan ma yamutu ne kawai yasanar da itah”
Mam” d`anki bai mutu ba yana nan araye mana iya bakin kokarinmu na ganin mun ceci rayuwarsa.

Daga Fadin Haka yajuya.

“Yashige dakin”

Turus yaja yatsaya Ganin sa a zaune, kamar ba shine wanda dasu ko numfashi bayayi ba, kallon gefe da gefen dakin yafara yi Dan atuna ninshi ba mutum bane.

“A iya saninsa wannan gubar yakan dauki tsawon lokaci kafin yasake mutum, harya fara gane mutane.

Fita yayi cikin sauri dan kirawo sauran `yan uwansa likitoci, Ganin yanda yafita a gigice yasa hankalin Ummii dasauran sojojin kara tashi.

Ba’a dade ba yadawo da wasu likitocin guda uku abayansa.

Ganin su cikin sauri sun shige dakin yasa Ummii fashewa da wani matsanancin kuka, basu dade da shiga ba _afeeya_ tashigo Wanda ita kebin MG da yaronta zasuje excotion egypt ne tabishi, Sai kuma wannan abun yafaru shiyasa tabar yaron acan tayiyo nan asibitin, cikin tashin hankali.

Farkon isanta sun hanata shiga ne, sanda takira ummi taturo captain Ahmed yashiga da ita!!! Ganin Ummii na kuka ne yasa itama tazauna ta fashe da nata kukan, bame lallashin wani.

Sai wajan 6 :00am mai martaba suka shiga asibitin, lokacin da suka isoh sun wuce gidansu dake nan Dubai “wato gidan Ummii sanda suka biya bashin sallolin da ake binsu, sannan suka nufee hospital din.

Ummii na ganin isowar mai martaba tatashi dasauri taje ta rungumeshi, sannan tafashe ta matsanan cin kuka, tana cewa sun kashe manashi, abinda take nana tawa kenan, bubbuga babanta mai martaba yahau yi, Dan Shima Idan yace zaiyi magana toh tabbas zai’iya yin kukan.
Allah kadai yasan yadda yakeji, sanin dansa dayafiso yana cikin wani hali,
Wani irin bakin ciki ne yatokare zuciyan kilishi jitakeyi kaman ta shakesu.

To be continued

_Ur’s_
_z33yyb3rw3r_

*BIBIYATA AKEYI*
_
_Bismillahirahmanirrahim_

_
Writting by
© _zaynab_ _bawa_
( _z33yyb3rw3r_ )

*Dedicated* *to*

Leave a Comment





No one has commented yet. Be the first!
Leave a Reply