Bibiyata Akeyi Hausa Novel Hausa Novels

Bibiyata Akeyi 74


Bibiyata Akeyi 74
Viral

Page 74

Washe garii *hanna* tataashi dasauk’in damuwarta, amma wani shafin na zuciyarta yana fargaban halinda yake ciki, idan kuma tayi tunanin hakan Sai tayita addu’a.” hartajii sanyii acikin zuciyarta, haka har aka shiga sabon satii.” anty afeeya kuma bata tafii ba, dan ita tafiso tatafii tareda *hanna* .” Washe garii tun sassafe *hanna* kwalliiya sosai ta shiga kitchen da kanta ta shirya masa abincii.” sosai tayi kyau.” zuwa yamma jikin *hanna* yayi sanyii sosai.” anty afeeya dake zaune agefe tana kallonta tun d’azu gabaki d’aya tausayinta yagama kamata.” ganin magrib ta doso yasa *hanna* tajuya ta kalli anty dake zaune cikin alamun karyewar zuciya, da rawar murya da sark’ak’iya tace anty haryanzu shiru bbu labarin dawowarsu.”
Girgiza kai anty tayi tace, a’a *hanna* kada kiyi kuka kinsan fa ba rana aka yankeba kuma ba sanarwa akayi ba, tom ki yi hakurii, amma kuma mujirra zuwa gobe tukunna, ai shiru *hanna* tayi batace komai ba.”
Har 10:00pm *hanna* afalo tana zaune sanda anty afeeya ta takura mata sannan tashiga takwanta.”
Washe garii ma tun sassafe *hanna* ta tashi tafara aiki, kamata jiya sanda yagama komai sannan tashirya cikin ran tsattsen less mai kyan gaske.” tayi kyau sabon y’ar rawar ta tafara buya,”
Anty afeeya da bata kallonta bbu abun da takeyi, duk tausayinta saiyabii yacikata.” yauma komar jiya *hanna* batayi baccin kirki ba.” sanda *hanna* ta shafin kimanin ten day’s tanayiwa MG shirin dawowa amma bbu shi bbu labarinsa, ita kanta afeeya sanda tayi danasanin k’arya da tayi mata nacewa zasu dawo, tayi hakanne duk dan ta faranta mata rai.”
Washe garii suna zaune afalo *hanna* tayi mata shi ta cinyan afeeya suna d’an ta6a hira, yana tace tafara ringing dake hannun *hanna*.” ganin wandabekekira yasa jikin *hanna* yayi sanyii, dan tana mijinta ne, ita kuma nata mijin batasan awani hali yake cikiba.” nan take mood nata yacanja.”
Batasan mai anty afeeya ke fad’a ba hankalinta baya jikinta.” tana gama wayar tadubii *hanna* wanda hankalinta baya wajan tace *hanna* shiru bata amsaba ta6ata tayi, firgitgit tataashi, Girgiza kai kawai anty tayi tace, *hanna* ki shirya yau muwuce nageria, abban adheel yakirani bayada lpy yanzu haka yana emergency, tak’arashe maganar cikeda tsantsan damuwa.” dasaurii *hanna* yatashi tace subhanallhi, anty tatashi tace anty adheel kuma?”
Eh *hanna* tashi ki shirya mutafii.” Girgiza kai *hanna* tayi hawaye na zirara tace anty kije kawai nikam zanjirashi.” Girgiza mata kai anty afeeya tayi tace, a’a *hanna* bazan iya barinki anan ba.” tana kuka tace Allah anty bazan iya binki ba, wallhy zanzauna najirashi har iya k’arshen rayuwata,” bayadda anty batayi *hanna* tabita ba amma tak’ii haka tana ganii takoma, ita kuma zauna zaman jiran MG.”

================

Karimace dake zaune tana yiwa abida masifa tace, wallhy nidai zantafii, kintsaya kina 6ata mana lokacii, kina so jimawa kad’an *mama tace tafasa.”
Itakuwa abida santa tagama iya shegenta sannan suka futa suka samu hafsat dake jiransu.” futa sukayi zuwa gidan anty, idan kagansu baza kace ba y’an uwa bane, iya kulawa ana bawa su karima, dan bbu wani bamabamcii, soyayya sosai suke samu daga iyalan gidan.” iyakacin soyayya mama tana nuna musu, duk kwakkwafin mutum bazai gane ba ita ta haifesu ba.” Itakuwa.” suma sun riqeta gamm tamkar mahaifiyarsu.”
Gidan suka nufa, suna shiga suka sami antyy maman amal nazaune, da sallama suka shiga abida tak’arasa gefenta da gudu tazauna.” dan jininsu yahad’u sosai.”
Rabon najeeb da gidan anty, tun auren *hanna* dan fushi yakeyi dasu daga ita har mijinta, aranar kawai yajii sha’awar zuwa gidan kai tsaye gidan ya nufa.”

============

Yau duk eatate yad’auka, gidan tv da radio Sai sanarwa ake da dawowan soldier’s gobe, ai kuma farin ciki da fargaba duk yataruwa *hanna* tanason ganin mijinta amma batasan awani hali zata ganshii ba, batasan yana raye ko baya raye ba.”

_Nacika alqawarii_

To be continued

Ur’s
Z33iiyyb3rw3r

*BIBIYATA AKEYI*

_Bismillahirrahmanirrahim_

Writing by
© _Zaynab Bawa_
( _z33iiyyb3rw3r_ )

_Like my page on Facebook :::Zaynab BAWA novels_

Followed me on instagram ::::mhiz_z33iiyyb3rw3r

*Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata agareshi yace duk wanda yakaranta* “`waraddal lahul lazhina kafaru bi zaigaizihim lam yanaluu khaira akafallahull mu’umininal qital wakanallahu qawiyan aziza“` *Allah zai kareshi daga sharrin kowani irin hallita,*

*Allah subhanahu wata ala yana cewa, wala’iin shakartum la’azidannakum, yace idan kuka godemin nikuma zan k’ara muku, yanada KYAU fad’in kalmar Alhamdulillahi domin nuna godiyarka GA ubangiji. Koda ace Allah yajarabceka ta wata hanya, alokacin faruwar abun kalmar Alhamdulillahi ne kawai yakamata tafito abakinka A wannan lokacii.” Allah yasa mudace ameen ya Allah*

================

Leave a Comment





No one has commented yet. Be the first!
Leave a Reply