Gurbin Ido Hausa Novel Hausa Novels

Gurbin Ido 47


Gurbin Ido 47
Viral

47

Washegari tare suka hada breakfast da baba tabawan,suna aikin suna taba hira,sanye take da wasu kayan bacci masu taushi sosai,saidai basu da wani kauri me yawa midnight blue da torches na olive color,wandon iyakarsa saman idon sahunta,rigar kuwa tsahonta iya cinya ne,short sleeve ce,don iyaka dantsenta hannun yatsaya,daga gaba rigar ta dan lafe mata,har tana fidda shade na brazier dinta,bata damu ba sosai,tunda tasan babu kowa a sashen daga ita sai baba tabawa,hakanan babu me shigo musu,kalar kayan ta fidda hasken fatarta sosai,kanta qaramin dankwali ne mai santsi data masa Vshape ta daure sassalkan gashinta,wanda santsinsa dana dankwalin suka hadu waje daya suka sanya dankwalin qin zama sosai a kanta,duk bayan minti biyu saita janyo dankwalin ta rufe gaban kanta dake da wani irin kwantaccen suma mai santsi data zagaya har qeyarta,duk da safiya ce,amma jikinta qamshin turaren women maze alharamain yakeyi,qamshin dake cakude dana body mist datake amfani dashi.

Hira suke sosai,baba tabawan tana bata labarai wadanda maimunatun take jinsu daban,saboda sun saɓa da tata rayuwar,saidai hirar tana nishadantar da ita sosai,saboda ko a saman fuskarta ya nuna hakan,kyawawan jerarrun fararen haqoranta sun bayyana.

Knocking suka jiyo,maimunatu ta tsame hannunta daga ruwan da take dauraye kwanukan da suka gama amfani dasu,ta goge jikin towel na kitchen din,sannan ta fito da niyyar budewa ba tare da tunanin komai ba.

A hankali ta kama handle din ta bude,abu na farko daya fara marabtarta qamshin jikinsa ne,wanda acn da aka balbalawa babban falon ke tunkudo qamshin da gaske zuwa nata falon.

Saman kanta idanunsa suka fara sauka,wanda dankwalin kanta ya zame xuwa rabin kanta,abinda ya bawa gashinta damar bayyana sosai,sai ya zame idanun nasa ya janyesu gefe,tasa dukka hannayenta biyu tana dafe dankwalin dake shirin faduwa daga kanta gaba daya,ta kuma janye qafafunta da taji suna sarqewa zuwa gefe ta bashi hanyar shigowa,a sace idanunta na binsa da kallo,cike da mamakin shigarsa ta yau ta zallar bahaushe,cikin wani lallausan farin yadi me shara shara,wanda hatta fara qal din singlet din dake jikinsa sai data bayyana,ya giftata ya bar mata qamshinsa wanda batasan me yasa take samun wata nutsuwa ta musamman ba duk sanda zata shaqeshi.

Kamar wata mara gaskiya ta rabe a bayansa

“Ina kwana?” Ta fadi a matuqar ta kure,nadamar yadda ta fito haka gaba gadi ba tare da tambaya ko sanin waye ba tana shigarta.

Gaba daya ya waiwayo zuwa inda take tsayen,hannayensa dunqule cikin aljihun rigarsa,ya zube idanunta da sukayi wani irin laushi saman qirjinta dake bayyana shatin baqar brazier dinta,yadda yake qoqarin janye idanunsa daga wajen haka zuciya da idanunsa ke ingizashi zuwa ga ci gaba da kallonta,yana jin kamar wani mayen qarfe aka dasa ma idanun nasa a wajen,yayin da wani abu me kama da tsarguwa ya saukarwa maimunatu jin shuru bai amsa ba,cike da jarumta da son tsira da mutunci ya raba idanunsa daga wajen yana lumshesu

“Karki sake irin wannan gangancin,kinsan waye da kk bude qofa batare da kin tambaya ba?” Yayi maganar yana sake qarewa shigarta kallo,hatta sambala sambalan qafafunta sun fito sosai saboda rashin tsahon wandon,yana kallonta ‘yar qarama a gabansa,yanayin da ya tuna masa da zamanin amarcinsa da shaheeda, she’s always like this……under eighteen,sannan taci gaba da zama da dabi’antuwa kamar yadda yakeso ta kasance masa,ta ina ta kuma yaya zai maida GURBINTA?.

“kayi haquri” kalaman suka sauka a kunnensa dai dai da irin yadda shaheeda take fada masa,bata kuma taba canza kalamanta da haka ba,koda shi ya bata mata,yakance

“Uhnnnn…..u are killing me shaheeda,ko yaushe kayi haquri?kayi haquri,You don’t want to make excuses for yourself?” Daga kai maimunatu da sauri tayi ta dubeshi jin abinda ya fada,sai shima ya maida idanunsa kanta ganin yadda take kallonsa,sai a sannan ya karanci ashe a sarari yayi maganar,saidai can qasan maqoshinsa ne,janye idanuwansa yayi yana dan tsuke fuska kadan,ya akayi maganar ta fito fili?

“Shaheeda” takira sunan a ranta tana son tuno inda tasan sunan,ummin amna?,kwanyarta ta bata…..kafin ta gama tantancewa muryar baba tabawa ta yiwa falon tsinke.

Sai a sannan ya dauke kansa da shanyayyun idanunsa gaba daya daga dubanta ya maida ga baba tabawa,wadda har tayi niyyar juyawa a yanayin data gansu a tsaye,cikin sakanni ta karanci wasu qananun abubuwa a fuskar kowannensu

“Manya,har an fito?” Kai ya jinjina ya kuma ranqwafa yana gaidata,ta amsa cike da kulawa,ya sanya hannunsa a aljihu ya fiddo kudi ya ajjiye mata

“Ah…..ai an kammala karin safe,ka jira a gabatar maka” bata saurari amsarsa ba ta juya ga maimunatu

“Suna kitchen fa” ta fadi mata,kamar wadda ke jiran umarnin barin wajen tayi gaba tana qara hanzari,gaba daya kamar tayi layar zana haka take ji,da so samu ne dakinta ya kamata ta biya ta fafa dauko hijabi,to amma kuma baba tabawan fa?,hakan zai zama kamar wani rashin girmamawa ne a gareta,dole ta wuce zuwa kitchen din.

Sanda ta dawo falon a tsaye ta sameshi yana saita agogon hannunsa,qarin tashin hankalin baba tabawan bata nan a falon,sau daya tak ya daga kai ya kalleta ya maida ga abinda yakeyi,saita wuce dining ta jera komai,kafin tayi magana taga yana takowa zuwa wajen,yaja kujera daya ya zauna a kai,har yanzun bai kuma dubanta ba.

“Me za’a zuba maka?” Tayi tambayar tanason riqe rawar da muryarta keyi,don gaba daya ta gama rudewa,Allah Allah take ta gama serving nasa tabar wajen

“Anything” ya amsata a taqaice,warmers din ta fara qoqarin budewa,saidai duk wadda takama zata bude saita kasa,saboda santsi da kuma yadda jikinta yayi weak,tako ina a jikinta takejin idanunsa na mata wayo,tayi Allah wadaran shigar da kuma yadda ta zauna haka yau din babu ko dan baby hijab din da take amfani dashi ko da yaushe,a nutse yake karantarta,kafin ya kauda idanunsa yana latsa wayarsa,ata qarshe ne ya daga hannu da niyyar karba y bude ganin ta kasa,incidentally hannunsa ya sauka saman nata hannun,abinda ya haifar masa da wani irin shock a jikinsa,yayin da ita kuma tashin farko jikinta ya dauki rawa,ta kuma zame hannun nata da sauri taja baya kadan,yi yayi kamar baisan abinda ya faru ba,a nutse ya dauki bowl da serving spoon ya fara diban farfesun kayan cikin dake cikin warmer din.

Tsoronta gaba daya ta dunqule ta kuma hadiye,saboda tuna warning nata daya taba yi,ta matso a kasalance,ta jawo flask na tea data hada da kanta da wasu hadin kayan shayi na musamman data shekaran jiya tana cikin browsing ta fara zuba masa,wani irin qamshi me dadi ya gauraye wajen,har sai da yaja iskar data kwaso qamshin har cikin hunhunsa,deep inside kuma yawunsa ya fara tsinkewa,ta dauko kwalin suger ta dauki one cube ta saka,ta sake debowa zata qara sanyawa kenan yace

“Enough,ya isa” gaba daya kwalin sugar din ya subuce daga hannunta don dama a tsorace take,suka fara rige rigen afkawa cikin kofin tea din,abinda ya bawa ruwan zafin damar yin fallatsi,ya dawo mata hannayenta,taja baya da sauri tana jin zafin saukar ruwan zafin na ratsata sosai har kwanyarta.

Spoon din hannunsa daya fara diban farfesun ya ajjiye,ya hade yatsunsa waje guda yana kallonta,ta hada gumi tana yarfar da hannun,da alama ruwan ya tabata sosai,har ya dauki spoon din xaici gaba da cin abincinsa sai kuma ya kasa,komai tayi shige yake masa da silly attitude na shaheeda data sha yi masa farkon aurensu

“seat here” yayi maganar yana jan kujerar dake daura dashi,idanunta da suka tara hawaye ta daga ta dubeshi dasu,kamar wadda ke shirin sakin kuka,sai ta tako a hankali kamar kazar da qwai ya fashewa a ciki,ta zauna a darare saman kujerar tana dubansa

“Let me see” ya fada yana miqa mata hannunsa,idanunsa cikin nata yana kallon yadda ta narke gaba daya,gumi kuma ya tsatstsafo saman goshinta.

Sai data maida dubanta ga lallausan tafin hannunsa kamar me tsoron wani abu,sannan ta miqa masa hannun nata a hankali,ya miqa nasa ya riqe yatsun nata.

Qaramar qara ta saki da siririyar muryarta me zaqi wadda ta ratsa dodon kunnensa da kyau,idanuwansa ya rintse sosai sannan ya budesu ya zubesu saman fuskarta wadda tuni hawaye sun fara mata zarya,ya dinke fuskarsa tsaf yana ci gaba da tsare gida

“What is that?,zaki kashemin kunne ne?” Kai ta girgiza,gaba daya hawaye ya wanke mata fuska,ta wani narke cikin wani yanayi daya darsa tausayinta cikin ransa,sai ya janye idanunsa yana qoqarin kawar da wannan ya mayar kan hannun nata.

Da sauri ya janye yatsunsa daga inda ya riqe din,saboda yadda wajen yayi jaa,da alama a wajen ta qone din,kafin yayi wani abu baba tabawa ta iso

“Lafiya dai ko maimunatu?” Tayi tambayar tana dubanta

“Subhanallahi” baba tabawan ta fada sanda taga hannun nata

“Garin yaya?” Ta jefa mata tambayar,rashin sanin amsar da zata bata yasa ta maida dubanta ga ja’afar,dauke kansa yayi kamar baya wajen,kamar bashi take kallo ba,kujerarsa ya sake jawowa gaba kadan,ya zamana dab da ita sosai

“Silly girl” ya fada qasa qasa,sake mele baki tayi zata sake sakin kukan,kamar yasan da haka ya kuma daga shanyayyun idanunta acikin nata,sai tayi hanzarin kulle nata idanun,ita kadai tasan me yake haifar mata idan ya mata irin wannan kallon,yana qara mata razani a kansa da kuma wani irin kwarjini da takeji kamar zai sata narkewa a wajen.

Sannu baba tabawa ta matso tana mata sanda ta duqufa yana mata tofi a hannun nata,ya kwashi kusan minti talatin yana mata tofin babu tsayawa,sannan ya zare hannunsa daga cikin nata

“Sannu maimunatu” baba tabawa ta fada fuskarta na nuna alhini,idanunta akan hannun nata da yayi jaa abinka da farar fata,kanta ta gyada

“Ko za’a kaita asibiti?”
“no need,bazai komai ba….in sha Allah,zanma hisham magana,zai prescribing mata pain killer,sai a kawo,she will be okay”

“To Allah yasa”baba tabawa ta amsashi,duk da bata gane komai da komai da yake fada ba

“Ki cire hijabin kisha iska” baba tabawa tace da ita,sai ta noqe taqi motsawa,ta yaya zata fidda hijabin data saka saboda yiwa jikinta shamaki,ya fuskanci sarai saboda shi din taqi motsawa,sai ya miqe kawai yana kwashe wayoyinsa ya xuba a aljihunsa

“Manya….ai ba abinda kaci” kai ya gyada

“Am okay,thanks” daga haka ya juya yana barin falon,yana kuma sanya hannunsa a aljihunsa yana laluben key din motarsa,don yau a masallacin wuro bokki yakeson yin ssallar juma’a,yanason kuma samun gaba gaba,ya tabbatar abbi ma yana ciki yanzu haka.
[11/24, 10:10 PM] Safiyyatulkiram:

Leave a Comment





No one has commented yet. Be the first!
Leave a Reply