Gurbin Ido Hausa Novel Hausa Novels

Gurbin Ido 64


Gurbin Ido 64
Viral

64

Da murmushi suka dubi juna ita da fatiman,ta bata hannu sukayi musabaha sannan suka fara gaisawa,fatima na matsa mata gefenta ta zauna,amna na saman qafafunta.

Cikin mintunan da sukayi suna jiran lokacin tashinsu ta sake sabawa sosai da fatima,kamar su dauki shekaru tare,tana da sauqin qai da kuma yawan hira,ta dauki maimunatu kamar mate dinta,duk da ta bata aqalla shekaru uku,don ita ta rufa shekara ashirin,wannan yasa maimunatu ta sake sosai,suka shiga hira da fatiman,suna baiwa juna labarin makaranta,duk da fatiman ta gama secondary school,yanzun haka tana 200level ne.

Tare da fatiman suka shiga jirgin,sai itama ta duba jikin boarding pass dinta kamar yadda taga fatima tayi ta laluba seat number dinta.

A hankali take dubawa har ta iso gurin,tuni daya kujerar wadda ita ke bakin window me ita yana zaune akai,saita juya tana duban inda su fatima ke zaune,ita da amna ne seat number dinsu daya, jabir kuma da ja’afar wadanda seats daya ne suka rabasu,batasan tsarin jirgi ba,tunda ba sabawa tayi da shiga ba,don haka ta zame qaraman jakar dake kafadarta ta zauna saman kujerar bakinta dauke da bismillah.

A hankali ya waiwayo yana dubanta,matashin saurayine wanda duka duka bazai wuce shekara ashirin da bakwai ba,kana kallonsa zakasan wayewa da hutu sun ratsashi,unexpected ya ganta a kusa dashi,sai ya tashi ya zauna sosai idanuwansa a kanta,duk yadda yaso basarwa amma ya gaza,cikin muryarsa dake nuna zallan iyayi yace

“Sannu ‘yammata” a hankali ta waiwaya ta kalleshi,sai ta dauke kanta tayi gyaran murya kawai ba tare da tace komai ba, shima sai yayi shurun,amma kuma lokaci lokaci yana waiwayowa ya kalleta,saidai ta basar,ta kuma tsuke fuskarta da kyau,kamar yadda ko sau daya bata waiwaya ta dubeshi ba.

Tunda ta zauna a seat dinta ya fuskanci wanda yake abokin xamanta hankalinsa ya gaza kwanciya,kunnuwansa naga jabir ne dake ta masa bayanin wasu receipt da suka biya kudin wasu clearance a wajen custom’s,saidai dukka hankalinsa yana kanta.

A hankali yaji kamar ana matsa zuciyarsa sanda ya fahimci saurayin yana yawan juyawa yana kallonta,ya dinga qoqarin dannewa da kuma kauda hankalinsa amma sai ya gaza,agogon hannunsa ya daga ya kalla,akwai awa kusan biyu a gaba kafin jirginsu ya sauka a lagos,sai yaja wani dogon tsaki,abinda yaja hankalin jabir kenan,sai a sannan ya fahimci bama fahimtar bayanin nasa yake ba,yakai idanuwansa inda ja’afar din ke kallo,sai a lokacin ya gane abinda ke faruwa,cikin taqaitaccen lokaci jabir ya qare masa kallo,hatta zamansa bai zauna properly ba,kamar wanda taushin kujerar bai masa ba,amma da alama duka bai fuskanci hakan ba shi.

Gimtse dariyar dake son qwace masa yayi,ya buda baki zaiyi magana dai dai lokacin ja’afar din ya dunqule hannunsa ya buga a hannun kujerar da yake kai

“It can’t” ya fadi yana miqewa zumbur,ya taka a hankali ya fito daga inda yake ya nufi wajensu.

Cikinsu ba wanda yasan da wanzuwar tasa a wajen,dai dai sanda saurayin ke qoqarin miqa mata tissue ganin ta rufe bakinta atishawa nason fita,ido hudu sukayi da ja’afar dake tsaye a kansu,ya goye hannuwansa a qirjinsa ya zuba masa wannan idanun nasa dake saurin ladabtar da kowa,wasu kibiyoyi da baisan suna fita a idanunsa ba nata spark.

Sosai kallon da yake masa ya dakeshi ya kuma yi masa kwarjini,sai ya janye tissue din bakinsa na subucewa da cewa

“Lafiya?” Cikin fargaba tare da tunanin qila matar aure ce kenan,tunanin da baizo ransa ba sai a lokacin,maganar da yayin tasa maimunatu daga kanta,suka hada ido,sai ya mata inkiyar ta tashi,yayi gaba,ta miqe tana sake saqala jakarta ta biyo bayansa.

Kafin su iso jabir har ya miqe yabar mususeat din,dariya kaman zata kasheshi,ya koma inda ta taso din,saidai koda hakan shima ya taya J dinsa kishin da yaketa qaryata kansa bashi yakeyi ba,ya dubi matashin

“Ku dinga hankali da matan mutane” ya fada yana jifansa da wani kallo me kama da harara,don shi din dama yafi ja’afar magana.

Shi daya ya dinga quncin rai,yaja tsaki yafi a qirga,ita dai bata dashi komai ba,har awannin da suka rage musu ya cika jirgi yayi landing a lagos cunkus dakin tsumma.

Motar kamfaninsa ta nan lagos ce tazo daukarsu wadda aka tanadar masa saboda irin haka dama sauran mamyan baqi da sukeyi daga qasashen waje abokan kasuwancinsu,already jabir ya musu booking na dakuna a daya daga cikin five star hotels,wanda kuma yafi kusa da inda sukazo duba ayyukansu,ciki da falo ya kamawa su ja’afar saboda amna,shi da fatinsa kuma single room.

To tun saukarsu lagos basu samu zama sosai ba,idan motar company tazo ta saukesu tun safe sai dare,wannan ya bawa su maimunatu damar yawo sosai cikin garin lagos,jabir yasa wata motar daga company musamman take zuwa duk sanda suka gama shirinsu ta daukesu tayita zagayawa dasu guraren shaqawatawa kala daban daban,ya tura musu enough kudi ta account din fatima,ga kuma bandir da J ya ajjiye mata itama,basu da wata matsala ta komai,duk yadda maimunatun tayi tsammanin ba zataji dadin tafiyar ba sai abun yazo mata akasin hakan,taji dadin garin fiye da zatonta,sunyi yawo sosai,hakanan fatima ta musu siyayya mai yawan gaske,musamman maimunatu da batazo da wasu kayan ba,saidai kuma ita fatiman kusan duka qananun kaya ne siyayyar nata,sai sakakku da zata iya fita dasu cikin gari,don haka maimunatu ta ware kowanne jaka daban,wandancan da takejin ba zata iya fita dasu ba,da kuma wadanda zata iya sakawa.

Duk yadda garin ke mata dadi amma bata mance da lissafin lokacin komawarsu makaranta ba,sunyi waya da afrah itama tana sake tuna mata

“Allah ya nuna mana,amma bana gida ma,muna lagos,kuma banga alamun dawowarmu ba” dariya sosai afra ta sake

“Wannan abu yayi min dadi,tsuntsun soyayyar ya fara sauka kenan,honeymoon aka tafi ne?” Kamar tana gabanta saita saki harara

“A’ah milkmoon aka tafi,tare fa muka tafi da amna,harda su fatima”

“To sai me?,bikin magaji zai hana na magajiya ne?,amna ina ruwanta?,zatafi kowa son a bawa daddynta kulawa,fatima kuwa na tabbatar saidai ta tayaki,kuma nasan ba daki daya kuke ba,kidai zauna garin kallon ruwa kwado yayi miki qafa”

“Mtsweew,Allah ya shiryeki afrah,gwara hajja tayi miki aure ta huta”

“Wallahi ko gwara a aurar dani a huta,idan ba haka ba…….”

“Ba’a kunne na zaki qarasa wannan zancan naki ba,ya girmi kunnuwana” saita datse wayar tana dariya.

A hankali ta aje wayar a gefanta

_ki tsaya dai kallon ruwa kwado yayi miki qafa_,wai me yasa kowa maganarsa kan ja’afar ne,kowa kusan abinda yake fadi mata kenan idan irin wannan zancan ya hadusu,sai ta sauke ajiyar zuciya,idanuwanta na hango mata kalar soyayyar jabir da fatima,wata irin soyayya me nuna zallar kulawa da kuma shaquwa,ita kanta abun yana burgeta,sau tari idan ya kirata bayan ya fita tunda yawancin lokutta suna tare,sai tayi kasaqe tana sauraren kalar hirarsu,ta fahimci ita kanta fatiman ta gano kalar zamansu,don wani lokaci ta taba cewa da ita

“Shi namiji da kike gani,babu abu mai sauqi wajen sarrafawa irinsa,sau tari dama suke nema ko jira ka basu,mijinki ko?,hmmmmmm,astagfirullah,soyayyarsu ta dabance,duk sanda suka tashi nunawa mace soyayya za’a sha mamaki,saidai suna da wani irin aji da kamewa,wanda zaisa ki gaza fahimtar inda suka dosa” ajiyar zuciya ta sauke tana gyara kwanciyar rub da cikin da tayi saman kujerun falon,amna na daki tana bacci,dama a ciki suke kwana ita da ita,shi ya canjesu a falon.

Qarar security na jikin qofar taji,kafin kuma ta ankara an murda handle din an turo qofar,sai ta daga kai da sauri don ganin wanda ya shigo din,saboda ta san wannan ba shine lokacin dawowarsu ba,zata iya cewa tun zuwansu tsahon kwanaki takwas yau,sau uku kawai suka hadu ita dashi,tana qunshe a daki sanda zai fita,kafin ya dawo ta tattare tayi kwanciyar barci abinta.

Tun kafin ya saki handle din idanunsa ke manne a kanta,wata gown ce a jikinta ta wani material maras nauyi,wannan yasa kwanciyar rub da cikin da tayi ya bayyana mazaunai da qugunta sosai.

A hankali idanuwansa suka kai kai,ya lumshe idanunsa tsigar jikinsa na zubawa,sai ya juya ya maida qofar ya rufeta,sannan ya soma takowa cikin dakin bakinsa dauke da sallama.

Tuni ta miqe ta zauna kanta a qasa tana wasa da yatsun hannunta,itakam dawowarsa a yanzun kamar takura ce a wajenta,dole saidai ta koma daki tayita zama

“Sannu da zuwa” ta fada a hankali tana miqewa tsaye duk da bataji ya amsa ba,taku biyu tayi taga ya babbake gaba daya hanyar wucewarta,idanuwansa a kanta,yau din kallonta tsakiyar idanuwanta yake kansa tsaye,ya karkatar da wuyansa gefe daya yana son hukuntata da idanun kamar yadda ya saba

“Am…zan zan wuce” ta fadi muryarta nadan rawa,saboda jiki da zuciyarta da taji sun fara amsawa

“Idan naqi fa?” Ya amsa mata yana hade fuskarsa,mamaki amsar da ya bata ta bata,sai ta dan tsuke bakinta kadan kafin ta sakeshi,idanuwansa suka kai kai,ya sake jin wani abu na sauka a dukka sassan jikinsa,yana kuma gauraya da gajiyar daya kwaso,idan yace pink lips dinta basa burgeshi yayi qarya,qara taku uku yayi qwarara sai gashi a gabanta jikinsu na gogayya waje daya,kafin ta qara wani tunani ya sanya hannuwansa ta baya ya dorasu saman mazaunanta,take a kuma lokaci guda kowanne numfashinsa ya fara barazanar daukewa na wucin gadi,namiji ne shi tsayayye,ita kuwa mace mai rauni,wannan yasa fa gaza tsaiwa a muhallinta ta fada jikinsa gaba daya,kafin ta samu ta fusgo numfashin nata,ta fara qoqarin raba jikinta da nashi,amma tayi latti,don ya zagaye bayanta da hannuwan nasa gaba daya.

Ji yake kamar an jan jininsa da na’urar lantarki mara zafi,wani irin shock yakeji sosai,gudun zuciyarsa ya fara rawa

“Hope ba da irin wannan kayan kike fita ba?” Yayi maganar yana dagata daga jikinsa,muryarsa na wani irin fusga,kamar zata narke a wajen haka takeji,kanta a qasa ta gyada masa kai,fiye da rabin hankalinta yana kan qofar daki,kada amna ta fito,ilai kuwa sai ga qaran qofan bude dakin,ba tare daya juya sashen ba yaja da baya ya sulale saman kujera

“Hadamin ruwan wanka” ya bata umarni karo na farko kenan,don da kansa yake hadawar.

Kamar qafafunta ba zasu iya daukanta ba haka ta jasu tayi ciki,amna kuma ta fito tana masa sannu da zuwa,a jikin bangon toilet ta jingina bayanta bayan ta kunna ruwan tana jiran na dumi ya sauko,kowanne sashe na jikinta ya zama week,wai me yasa?,me yasa irin hakan ke faruwa da ita?,tuno irin wani sassanyan qamshi gami da laushin daya ratsa fatarta tayi lokacin da ta isa ga jikinsa,kawai sai ta goye hannayenta aqirji tana matse jikinta waje guda kamar me jin sanyi.

Ta gama hadawa ta juyo ta kama handle din da nufin bude qofar sai aka rigata shigowa,ja’afar dinne,sanye da trouser dinsa da fara qal din singlet dinsa kamar ba’a sanyawa jiki ita,ya cika qofar ya kuma taho gaba daya,so babu wani space da zata rabeshi ta fice,dole ta janye da baya har ya shigo,idanuwanta na kallon qasa,don ba zata iya kallonshi a haka ba,tsoro yake bata,gaba daya dantsensa wasu irin muscles ne dake nuna yadda ya qware wajen motsa jiki da kuma daga qarfe,daga hannuwansa zuwa qirjinsa duka sun bayyana albarkatun gargasar dake tattare da wajen.

Ta dauka zai janye mata ne,sai taji ya maida qofar ya rufe,ya kuma fara zare singlet din da tayi saura a jikinsa,da saurinta ta qara gaba tana yunqurin bude bandakin,saidai ya saka lock a jiki,ta saka hannunta zata murza ta bude,ta tsinci husky voice dinsa na mata gargadi

“Karki sake ki budeni,am taking bath” tashin hankali,sai taja da baya ta sake jingina da bangon zuciyarta na wani irin bugawa cike da tsoro,to wanka zaiyi itama wankan akace masa zatayi?,tsoro ya sake kamata ganin yana zare trouser din jikinsa,ta rasa a wanne side zata tsaya ba tare da taga kominsa ba?, kowanne sashe na bandakin glass ne da zai baka damar ganin abinda ke faruwa a kowanne bangare da bandakin,kota juya ma gabanta glass ne,idan kuma tace shi zata fuskanta ba?,inaa,ba zata iya tsaiwa gabansa bama,sai ta runtse idanuwanta gaba daya hawaye na taruwa cikin idanun nata.

Rufe idanuwan nata ya bashi damar kallonta son ransa,ba abinda yake fuskarsa irin qirjinta dake cike sosai,ya kuma zauna ta cikin rigar saboda wata tattarar roba da aka yi mata daga sama, qaramin murmushi na gefan baki ya sake sanda ya fidda trouser din saboda yadda yaga ta cuno baki gaba,komai nata akwai childishness a ciki,some times ba abinda take tuna masa illa lokacin amarcinsu irin wannan shida shaheeda,tana tuna masa abubuwa masu yawa tattare da ita,ko a yanzun sai yake gani kaman ita dince.

Rataye trouser din yayi,pants na maza ne kawai ya rage a jikinsa

“Miqomin sponge” kamar ya mata tsawa a tsakiyar kanta haka taji,ta yaya zata iya bude idanuwanta ta kalleshi a haka?,sake maimaita mata yayi,sai ta fara tattakawa a hankali tana lalube ba tare data bude idanunta ba,qaramin murmushi ya qwace masa ganin ta saba hanya,tana ta lalube har arean da yake tsaye,sai ya zuba mata ido ya rabu da ita,baice mata komai ba har zuwa sanda ta damqi hannunsa.

Saki taso yi da sauri amma cikin zafin nama ya riqeta,ya kuma janyota cikin jikinsa gaba daya,yayi mata rumfa da yalwataccen qirjinsa,ya kuma lullubeta da tattausar fatarsa,matseta yayi sosai cikin jikinsa wani numfashi mai nauyi yana qwace masa ba tare da ya shirya ba,wani irin body contact ya samu da ita irin wanda bai taba ba,tudun mazaunanta ya taba sashe mafi kima a jikinsa.

Rasa abinda zatayi yasa gaba daya ta qanqameshi ta cusa kanta cikin qirjinsa bayan ya juyo da ita suna facing juna,hawayen da take boyewa suka sauka suka fara ratsa gargasarsa suka tadda fatarsa,dagata yayi kadan daga jikinsa yana duban fuskarta daya danyi jaa,ya lumshe idanuwansa da suka fara sauya kala saboda wani abu data harbawa kowanne sashe na jikinsa,siraran lips dinta na motsawa a hankali,sai ya sanya fuskarta a tsakiyar tafin hannunsa yana ci gaba da kallon labbanta,baya jin yau zai iya skipping komai da komai,for now yana jin komai nasa yana developing,kamar ana dawo da old version ne na ja’afar daya dade da bacewa wasu shekarun baya da suka shude.

Shi kansa baisan yadda akayi ba ya tsinciki labbansa saban nata,yadda ya zacesu haka ya samesu,da wani irin dumi da kuma sulbi don bazaice taushi ba,abinda ya sake tabashi kenan sosai,ya kuma haukatashi sai yayi amfani da harshensa ya buda bakinta sannan ya zura harshen a ciki.

Wasu irin hot kisses daya jima da kashesu a duniyarsa ya dinga bata,ciki da wajen bakinta ba inda bai tsotse ba,da zafi zafinsa yake aiwatar da komai,zafin da ya bayyana har cikin fitar numfashinsa dake sauka saman hancinta,take kuma shaqarsa zuwa huhunta,tana fiddo masa da nata numfashin shima yana aikawa nasa huhun,abinda ya sake haifar musu da wanu irin dimuwa gaba dayansu,gaba daya ta gama rudewa,jikinta duka ya dauki rawa kamar wadda zazzabi ya kama,wani irin baqon yanayi ne da batasan dashi ba,bata kuma taba kawowa zai risketa ba,ta sanya hannunta itama gaba daya ta kama kansa ta riqe tana son janyeshi daga fuskarta,saidai bata da wannan qarfin,ta rasa yadda zata rabashi da kanta kamar ma sake shige mata yake,kawai saita saki hawayenta suka soma zuba sosai.

Danshinsu ya taba fuskarsa,ya kuma sanya a hankali komai ya fara sakinsa,ya zare bakinsa a hankali,yana kuma dawowa cikin hayyacinsa,a nan ya tuna me ya aikata?,tsananin qarfin hali irin na namiji sai ya hade fuskarsa bayan ya janyeta still yana dubanta
[11/24, 10:10 PM] Safiyyatulkiram

Leave a Comment





No one has commented yet. Be the first!
Leave a Reply