Gurbin Ido Hausa Novel Hausa Novels

Gurbin Ido 73


Gurbin Ido 73
Viral

73

Kamar wancan karon,wannan karon ma ta dandana kudarta,duk da bai qarasa gamuwarsu ta farko ba amma taji a jikinta,harshi kansa yayi tunanin anya ya gama bude hanyar wancan karon kuwa?,rashin ganin jini yasa ya fahimci wancan karon ya kammala aikin nasa,wataqila ita din irin matan da sai a hankali suke gama samuwa ne.

Wannan lokacinma shi yayi barnarsa ya kuma shiga gyara,hawaye kawai takeyi tana jin yadda yaketa bata haquri gami da jero mata sannu,can qasan ranta tana mamakin yadda duk sanda hakan ta faru yake zama wani iri,kamar wanda ya aikata mummunan laifi,saida data tuna dabi’ar tausayi da shaheeda ta zayyanar akansa,sai mamakin nata ya ragu.

Yadda ya dinga kula da ita yasa ta sassauta qananun kukan da take masa,zazzabi yaso rufeta yau din ma,amma kuma ya hana afkuwan hakan ta hanyar bata paracetamol,ya kuma lullubeta a qirjinsa kamar first night dinsu,suka sha baccinsu sosai bayan sun hada azahar da la’asar data riskesu a farkon lokacin shigar mukhatarin la’asar din.

Basu tashi ba sai bayan magrib,ya sake wanka sannan ya hada mata itama,yace zaije yayi sallah ya dawo,haka ya fita yana waigenta kamar zata bace masa.

A inda ya barta a nan ya dawo ya taddata zaune,qarasowa yayi

“Lokacin sallah fa” idanunta fal da qwalla tace

“Bazan iya tashi ba….waj….wajen akwai zafi” sumar kansa ya shafa da kyau yana fadin
“oh sorry” ya tako a hankali zuwa inda take din,tsugunnawa yayi a gabanta kamar me shirin yin kneel down,ya kuma kama kunnuwansa da hannayensa guda biyun

“Laifin abban amna ne,a yafe masa” nauyi sosai ya aza mata ganin yadda ya zube a gabanta,sai ta boye kanta a kafadarta,tana jin ba zata iya hada ido dashi ba

“Yes,na gaji da ganin amna a haka,she needs a sister….”

“Na yafe” ta furta da sauri don kada yaci gaba da fadin maganar da fadin maganar da bazata iya dauka ba,murmushinsa dake bata mamaki da kuma jan hankalinta ya qwace masa,sai ya faki idanuwanta yayi wuf da ita sai bandaki.

Yanzun ma shi ke tayata,duk da yadda take noqewa,kusan dai shima sabon wanka ya sake sannan suka dawo dakin,ya saka kayansa da sauri saboda jun bell tana kadawa ya fita ya barta a wajen bayan ya nuna mata inda zata samu kayan sawa.

Dukka side din sabbabin suturu ne na mata,ta fidda guda ta saka,tana jin jikinta ya mata dama dama,sannan ta janyo wayarta data hanga qasan gado ta kunna,low battery ta nuna mata ta sake mutuwa da kanta,saita matsa gefan gadon ta sanya mata charge ta koma ta tada sallah.

Har ta idar bai shigo ba,wannan ya bata damar kunna wayarta,umna sa’adatu ce a ranta,so take taji muryarta,tana gama kunnawa kuwa kiranta ya shigo,ta saki murmushi tana dagawa

“Diyam dita…..ina kika shiga yau duka wayarki a kashe?,na kira ammanku tacemin dazu kuka bar gidan,yanzu nake shirin insa driver ya kawoni gidan naki naga ko lafiya,hankalina naji ya tashi” murmushin jin nauyinta ta saki,ta rasa me zata ce mata,wacce amsa zata bata,Allah ya taimaketa dabara ta fado mata

“Wayar ne charge dinta ya qare,ban kuma kula ba sai yanzu”

“To alhmdlh” hira suka dan taba kadan,kasancewar ba wani sabo bane mai yawa tsakaninsu ba abun tattaunawa sosai,ta tambayi su fareeda,sai ta miqawa su faridan waya,suka gaisa,umma sa’aden ta karba wayar tace zatayi sallah zata sake kiranta.

Tana sauke wayar yana shigowa,bakinsa dauke da daddadar sallama,sai ya tuna mata zamansu na johannesburg,yadda ya iya rera karatun qur’ani kamar wani baqin balarabe,muryarsa nada dadin ainun,sau tari da sautin karatun qur’aninsa bacci yake sake saceta,tana son muryarsa a guraren guda biyu,yayin karatun qur’ani da kuma sanda yake sallama.

Samun zuciyarta tayi da wani irin bugawa,ta lumshe idanunta tana amsa masa sallamar,qarasowa yayi ya zauna daga bakin gadon yana fuskantarta sosai,sai ya miqa mata hannunsa ya mata alama kan ta taso,murya can qasa kamar yadda ya saba yi mata magana yace

“Zo muji jikin naki”a nutse ta miqe tana isa gabansa,shirin zamewa ta zauna tayi sai ya janyota ta fada jikinsa,yayi mata masauki akan cinyarsa.

Hannunsa ya sanya ya shafi wuyanta,saita karyar da kai gefe tana jin tsigar jikinta na zubawa

“Thank God,babu zazzabin,ki qarasa shiryawa mu fita ki tattaka ko zaki sake warwarewa,amma inajin yau saidai mu kwana a nan ko?” Ido a narke ta dubeshi,sai yaji kamar ta watsa masa qanqara,yana masifar son shagwabar nan tata

“Uhmmm,kamar akwai magana a bakinki,say it…. Don’t be shy” da gaske kunyar tashi takeji,sai ta boye kanta a kafadarsa sannan tace

“Bazan iya tafiya ba” har cikin b’argonsa yaji maganar,don sai da yaja numfashi sosai,maganar ta shiga kunnensa da yawa,kamar tana sane tayi hakan

“Zaki iya…..am by your side,i will support you” ya qarashe maganar yana dagata sosai.

Laffaya ya fidda mata a side din kayan dai data dauko,ta riqe masa ya daura mata,data kalli kanta sai taga kamar ba ita ba tsaye gaban mudubi

“Me yasa kika goyi bayan maganar anni akan tawa uhunnn?” Shuru tayi masa ba tare data iya amsashi ba

“Well,bakya tausayina….kuma bakya sona ko?” Salon da yayi maganar a narke yasa dole ta daga kanta tana duban fuskarsa ta cikin mudubin,gaba daya ya koma kalar tausayi,tana mamakin yadda yake komawa haka a gabanta,why?….me yasa ne?.

Jin shurun ya sake biyo baya sai ya zagayo da kansa ta kafadarta,a hankali ya sakar mata kiss a kuncinta,sannan ya dawo da baya cikin kunnenta ya rada mata wata magana data sanyata sandarewa,sai ta rufe idanunta,matsananciyar kunya tana yawo da ita,maganar kuma naci gaba da amsa kuwa a kunnen nata

“U are very sweet fiye da duk wani abu me zaqi a duniya” anya kuwa ba matsala ja’afar din ya samu ba?,ita maimunatu yake gayawa wadan nan kalaman?.

Zaune kawai sukayi cikin mota ya dinga wani slow driving da ita manyan tituna tana more kallonta,kusan awa daya sukayi a haka,sannan ya zarce da ita wani babban wajen cin abinci me shegen tsada,babu mamaki tunda dama waje ne na wane da wane,ya bata menu ta zaba duk abinda takeso,sai ta rasa me zata zaba din,tunda dai ita ba saba fita tayi gurare irin wannan ba,uwa uba ma kuma bata iya cin abinci cikin jama’a ba tunda ta taso

“Duk abinda aka kawo maka” haka tace masa,to ko da aka kawo dinma juya abincin kawai take,yana ankare da ita,ya fuskanci kunya ne da ita sosai da sosai,yana shirin mata magana wayarsa ta dauki tsuwwa,sai ya aje spoon din hannunsa ya daga wayar.

Sallama kawai yayi ya tsaya yana sauraren bayanan da ake masa

“How comes?” Ya fada fuskarsa na bayyanar da bacin rai,ya sakeyin shuru kafin ya sake cewa

“Okay,thanks”.

Unaisa dubai taje?,an tabbatar kuma ‘yan gidansu da suka tafi tare dukka sun dawo?,a ina ita din ta tsaya?,wannan itace tambayar da ya jefa ma kansa,ta yaya ma zata dauki qafa zuwa wata qasa bada izininsa ba?

“Have you finished?” Ya tambaya maimunatu,sai ta gyada masa kai,ya kira waiter din ya aje musu kudinsu kan plate din ya qara gaba kafin ya qaraso ma,yana riqe da hannunta.

Shuru suke cikin motar yana tuqi,hankalinsa yayi wani waje na daban,itama hanya take duba ganin still yanzun ma ba gida suka nufa ba,ba wata tafiya sukayi.mai tsaho ba suka shiga wata unguwa,basuyi nisa ba ya tsaya qofar wani gida ya danna hon mai gadin ya bude masa.

Parking lot na gidan ya tsaida motar,ya waiwayo yana dubanta da idanunsa dake cike fal da bacin rai

“Ki shiga ciki,only one hour” kai ta gyada,duk da bata gane ina bane,bata kuma fahimta ba sai data kutsa kai falon gidan sukayi ido hudu da fareeda.

Karadinsu ya sanya umma sa’ade fitowa,murmushin fuskarta yaqi boyuwa,ta rasa inda zata tsoma maimunatu

“Amma kun shammaceni,ke dawa?”

“Shine ya kawoni” ta fada bayan ta rasa sunan da zata kirashi dashi,sai ta aike fareeda tace tace masa ya shigo,duk da ko a baya bai tana shigowa gidan ba,iyakarsa daga waje ne idan ya gama abinda zaiyi ya koma.

Ta samu bayanan,mai gadi ya shaida mata yana sauke baquwar yaja motar ya fita

“Ko kwana zakiyi?” Murmushi ta saki,itama zataso hakan inda zai barta,don ita yanzun tsoron kadaicewarsu ita dashi takeyi

“Baice hakan ba,inajin akwai inda zaije ya dawo” ta fada tana tuna mood din fuskarsa data gani tun a wajen cin abinci.

Dukansu suka hadu sai hirar tafi armashi,ta samu sunyi irin abincinsu nacan gida,don haka ta saki jiki sosai taci,sai data qoshi fareeda tana gyaran wajen umma sa’adah tace da ita

“Har yanzu babu labarin abbanki?” Cikin matuqar alhini da kuma kewarsa maimunatu tace

“Babu umma,Allah ma yasa yana raye” kai ta girgiza,cikin bata qwarin gwiwa tace

“In sha Allah yana raye,a yanzun ne zamuci gaba da addu’a da kuma nema,sannan shi kansa a yadda nasan shi a matsayin mutumin kirki,nasan duk inda yake hankalinsa yana kanku”

“Allah ameen” maimunatu tace tana sadda kanta,tana kuma tuna fuskar.mahaifin nata da har ta soma neman dusashe mata a ido.

Mintuna kadan ya qara a awa dayan ya dawo,ya aika ta fito,sai umma sa’ade tace ya shigo su gaisa mana,kememe ya qiya,don shi baya shiga gidan mutane haka kai tsaye,musamman idan mai gidan baya nan

“Ja’afar?,har yanzu haka yake kenan,banda abinsa nan din ai ba baqonsa bane,gidan babansa da mamarsa ce,muje na gaisa” umma sa’adah ta fada bayan ta hada ma maimunatu uban kaya,wai duka tsaraba ce aka ware mata nata,haka suka rakata mota niqi niqi.

Ko a hanya hannunsa na cikin tafin hannunta yana driving,yanata kuma amsa waya,batasan akan me yaketa wayar ba,amma kuma taji ya ambaci sunan unaisa kusan sau biyu,a haka suka isa gida yanata wayar.

A falo ta barshi ta shige daki,har ta gama shirin kwanciya ta kwanta bai shigo ba,bawai don tana saka ran zai shigo dakin ya kwana ba,sai tayi lamo tana jin gadon wayam,a sannan ne taji motsinsa,ya shigo riqe da wasu kaya,ya bude closet dinta ya zubasu,sannan ya shige toilet dinta.

Ya kusa minti talatin sannan ya bude ya fito,daure da bathrobe dinta,wanda ta tsaya masa iya qaurinsa saboda ya fita tsaho sosai,qamshinta dake manne jikin robe din yana ta shigar masa hanci.

Sassan da take kwance ya maida dubansa,sai suka hada ido tana satar kallonsa ta qasan duvet,da sauri ta runtse idanunta tayi kamar bashi take kalla ba,sai ya saki miskilin murmushin gefen bakin nan nasa,ya qarasa gaban mirror ya dauki lotion dinta,yana kallota ta cikin madubin

“Satar kallon nawa na meye kuma hajjaju?, just get up and look at your husband directly” kunya iya kunya ta kamata,saita shagwabe fuska ta kuma turo baki,ya hangota ta madubi,tsaiwa yayi cak da shafa man yana kallonta,yasan yanzu zata kasheshi da shagwabar tata

“Ni bakai nake kallo ba fa?” Sauke dukka hannuwansa yayi murmushi na subuce masa

“To wa kike kallo?” Sake tura baki tayi tana bata fuska,sai ya waiwayo ya nufota gaba daya,idanunta na rufe sai ji tayi an dagata,abinda ya sanyata ware manyan idanuwanta a kansa wadanda suka qara haske

“Ni ke nake kallo,kuma nakeso nayita kallo,jeki hadomin coffee” ya fada yans kallon light blue silk sleeping dress din jikinta,sai ya duqa a hankali yayi kissing qirjinta yana yaye mata duvet din,kana ya kama.hannuwanta ya taimaka mata ta sauko ta zura soft slipper dinta dake gaban gadon,yana tsaye yana kallonta har ta fice.

Numfashi ya zuqa ya fesar,wai dama haka kakejin wanda kakeso a zuciyarka?,yadda yakeji yanzun a kanta,bai taba din abu cikin zuciyarsa kwatankwacin hakan ba,qarasawa yayi ya gama shiryawa,sanann ya zura silk pyjamas dinsa navy blue,qirar kamfanin laurent.

Saman bed sofa ya koma ya zauna yana duba wayarsa, zuciyarsa cike fal da mamakin unaisa,baya son zarginta kan bin mazan banza,saboda yana tausayin mahaifinta,to amma kuma jikinsa yana yin sanyi idan ya tuna a inda ya fara ganinta,sannan kuma binciken da yasa aka masa ya nuna ita da wani ne suka koma,ya sake samun tabbacin hakan ta go and come ticket data siya,dama can ta shirya komawar kenan ba da sanin kowa ba?,zai zuba idanu yaga lokacin dawowarta.

Bayan ta kawo masa coffee din sai ya tsirar mata qananun aikin da dole tayita kai kawo,yayi relaxing jikin sofa yana qare mata kallo ta cikin sleeping dress din nata,har sai daya gamsu don kansa,sannan a zuwanta na qarshe lokacin ya kammala abinda yakeyi ta kawo masa turare,sai ya hade turaren da hannunta ya dorata saman cinyarsa.

Hannu yasa a tausashe ya fara zame mata rigar,wanda santsinta yasa ta fara fita ba wani wahala,sai tayi rau rau da idanu tana dubansa

“Sanyi nakeji”

“Kina da bargon da yafi wannan dumi…. you know what?, sleeping dress amfaninsu a wajen kadai kafin lokacin kwanciya barci ne,bana buqatarsu daga sanda zaki kwanta,i only need your skin,i really enjoy body contact” ya qarasa maganar cikin tsakiyar kunnuwanta,har sai data damqe hannuwanta waje guda tana rintse idanunta.

°°°°°°°°°Karfe uku da mintuna na yammacin washegari cikin makarantar tayi musu,bayan ya gama nuqu nuqunsa fes,kamar ma bazata koma din ba sannan ya baro office da kansa ya karba key ya daukota,bayan anni ta kirashi ta gaya masa,zata turo hisham ya dauketa ya kaita.

Fuska ya bata sosai,yana jin wani mugun kishi yana maqare masa wuya,yama rasa amsar da zai bawa annin

“Saiki shirya kayan tafiya asibiti jiyyarsa indai ya sake yazomin gida da sunan daukarta” haba ta kama,dariya nason qwace mata amma ta maze

“Iyyeee,dan nan?,dan daba ka zama,to wallahi ahir dinka da furta ta’addanci”

“Me kikeso ne nayi anni?,dole saikin qure haqurina……is okay,i love maimunatu……inason maimunatu,ina sonta……ina sonta,banason kowa ya rabeta please,karki qara wannan maganar anni, maimunatu tawa ce…..” Girma maganganuna nasa suka yiwa anni,taji tsoron kada ya baro babbar magana,tasan halinsa duk randa ya cika ya fara fidda abinda ke cikinsa baya ji baya gani,don haka ta dakatar dashi da sauri

“Kai arcannn,yi ta kanka yaro,bani zaka gayawa wannan zancan banzan ba,nidai a maidamin yarinya makaranta ehe” da sauri ta datse kiran,sai ya sauke wayar daga kunnensa cikin wata kasala kamar wanda aka yiwa dukan tsiya,yabi wayar da kallo yana murmushi kawai,yasan maganin annin,daga yau shima zai nuna mata dan zamani ne shi,tunda so take ta qure haqurinsa.

Gashi dai ya kashe motar,amma kuma bai bude motar ba,saima kwantar da seat din motar da yayi ya kashingida bayansa yana qare mata kallo,idanunsa a lullumshe kamar zai cinyeta,yana jin yadda zuciyarsa ke harbawa.

Jira taketa yi taji yace ta fita din amma shuru,daga inda take zaune ta hangi su afra sunyo arean riqe da qur’ani,da alama islamiyya zasu wuce,sai taji kewar karatun ta sake kamata,tana so ko iya yau a fara karatun da ita ta rage wasu kwanakin da tayi missing.

Har sukazo suka gifta su basu ankara da ita ba,suna ta hirarsu su ukun,saita dauke kanta zuwa gareshi,cikin sa’a suka hada ido

“Zan iya tafiya?” Kai ya girgiza mata alamun a’ah,sai ta shagwabe fuskarta as usual,wannan karon harda tabe siraran labbanta,ji yayi kamar ta saukar masa dafi a jikinsa

“My moon” ya kirata da wani.lallausan sauti,kamar wanda ya tashi a barci,daga kai tayi ta dubeshi,saiya miqa mata hannunsa ya mata sihn din tazo,ido ta fidda tana kallon gaban motar dake da farin glass,kowa zai iya hangosu,bata dauke idanunta ba taga coloured glass ya maye gurbin farin,kafin ta maida dubanta kansa ya fincikota ta fado kansa gaba daya.

Riqon tsauri yayi mata sosai,ya dinga aike mata da kisses kota ina,cikin wani irin zazzafan shauqi,ba inda bai kai harshensa a fuskarta zuwa wuyanta ba,cikin qanqanin lokaci dukka suka fita hayyacinsu,tuni ya zare hijab din jikinta yayi nasa waje

“I love you angel……i love you my moon…..i love you diyammm” shine abinda yake iya fada kawai cikin rarrabewar sauti,jikinsa na rawa.

Dan bugun motar da akayi yasa shi tsayawa cak,wasu dalibai ne da sukazo wucewa suna hira daya ta daki motar suka wuce abinsu,sakinta yayi a hankali ta sulale daga jikinsa ta koma seat dinta tana dunqulewa waje daya,yayin da shi kuma ya dora hannunsa cikin sumarsa yana yamutsata sosai idanuwansa a rufe bugun zuciyarsa nata tsere da sauri da sauri.
[11/24, 10:10 PM] Safiyyatulkiram

Leave a Comment





No one has commented yet. Be the first!
Leave a Reply