Bibiyata Akeyi Hausa Novel Hausa Novels

Bibiyata Akeyi 34


Bibiyata Akeyi 34
Viral

Page 34

 

*
Dakin yaya jalal tanufa, dirct, knocking kofan tayi, shiru akayi can takara, yaya is mee
Shiru nanma ganin haka yatabbatar mata yabayan juyawa tayi ta nufi dakin anty samha. ”

Shiga tayi tasamu anty samha sai waya takeyi batasanma tashigo ba, sai wani Kashe murya takeyi, biten din lower lips dinta tayi, sannan tayi shaking head dinta, arqnta tace, u always trying 2 seprate me from My very own, amma ke kinwani zage sai shan soyayyarki kikeyi, daki gane tafada, sannan tayi kwafa. ”
Gefenta taje ta zauna, chicks dinta ta tallafe da hannunwanta takura mata ido, dan d’aga wayar tayi akunnenta, d’aga mata gira d’aya tayi sannan tayi lowering voice dinta tace,” what happen dear?”
Shaking kanta tayi sannan tace bbu komai,” ok why d look?, ”
Kawai kunbirgenine, 👌 mayar wayan kunnenta tayi sannan tacigaba da phn dinta.”
Kamar wanda aka cikareta tace, anty da alama kinasonsa dayawa? ”
Shiru anty tayi for a while, sannan tamasa sallama juyawa tayi, tayi facing nata.”
Magana tacigaba, anty baki ta6a tunani kamar yadda kikeson yaaa abubakar, haka nekeson najeeb ba. ”
May be ma irinsonda nake masa yafi wanda kika yimasa.”
Wani irin tausayin *hanna* ne yakamata, a hankali tace iknw how u feel dear, but yakamata koyaya destiny dinki yazo kikarbeshi hannu bibbiyu, sai kikalla Allah yasaukaka miki. ”
Ahaka tayita rarrashinta har yamma suna daki suna tad’ii da anty samha batakarabi takan su amira ba.”

Najeeb na zaune adakin sa, tunani yakeyi yau kusan satii d’aya da yiwa abbansa magana, amma Shiru haryanzu, be nemeshiba, kuma bai bashi wata kwakkwaran evidence nakin zuwa nema masa aure ba.”
Gashi yarasa meyake damunsa ko waya ya dauka zaikira *hanna* sai yarasa dalilin sa zai hanashi.”
Wani iri yakeji wanda idan bai ganta acikin wannan week dinba sai ahankalii. ”
Yanke shawara yayi kawai zuwa nanda 2days zaije kano, dama already yasan address din.”

Umurtar sadam yayi daya tashi ya basu labarin MG. ”
“`Wai shin waye wannan MG d’inne daya addabemu kam??“`

*WAYE MG*

Abdullahi Abudulaziz lamido ne asalin sunansa.” asalin yan garin kano ne, masarutar kano.”
Kakansa shine sarkin kano mai rasuwa. ”
Abdullahi muhammad lamido, yanada yara shida,”
Abudulaziz shine babban d’ansa sai abudulrahman sai khadija da kuma halilullahi, sai hannatu da kuma autarsu sa’adatu. ”
Shekaran babansu talatin akan mulki Allah yamasa rasuwa, alokacinne Gashi babban d’ansa baiyi aure ba.”
Shine aka samu yar gidan k’aninsa mahaifinsa wanda yariga mahaifin nasa rasuwa. ”
Aka daura musu aure badan yana sonta ba.”
Sannan aka damka masa sarautar k’asar kano. ”
Mutane sunajin dad’in mulkinsa dan halinsa d’aya sak da mahaifinsa.”
Talakwa kai hadda ma masu kud’i suna yabawa kwazonsa. ”
Shekararsu d’aya da aure Allah ya azurtasu da yaro namiji, asaka masa isma’il sunan mahaifin kilishi, sosai yaron yariga ran mutane, magajin sarki.”
Iya gata yarima isma’il naganin gata sosai. ”
Alokacin tanada cikin secound born d’inne yad’auk’eta, zuwa dubai (abu dhabi) danyin shopping.”
Wani tamfasetsen shago sukaje dake cikin marina mall (abu dhabi) . ”
Shagon duk kasuwar yafisu girma, kowani kalan zinare kakeso awannen shagon daka sameta, duk prize dinsa.”
Nufan shagon sukayi dan sayan zinare, bayan sunshiga, ne kilishi tafara za6a. ” alokacin wata yar yarinya tashigo, wanda asa’anni zata Iya kaiwa kilishi, dan auren wuri akayiwa kilishi tuntana 15, gashi yanzu almost 3yrs da aurensu.”
Kallon yarinyar yatsayayi dan lokaci d’aya yaji yakamu da sonta luv at first side. ”
Hartagama abinda zatayi tafice, dawayo yabi bayanta, yaje yasameta, bata nuna kyankyaminsa nakasancewa bakar fata ba.”
Kwatancen gidan su tamasa be dauki lokaciba yaje dafarko iyayenta sunki yarda, hqr takaiga kullum, yana kofar gidan amma bbu mai kulashi. ”

Ita kuma Allah yadaura mata sonsa sosai, yadda kullum cikin kuka take.”
Takurin daya ke musu ne yasa suka yanke shawarar bashi amma sai sunyi bincike. ”
Binciken da sukayi ne ya nuna musu matsayinsa bakaramin mamaki sukayi na ganinsa babban mutum amma yake irin kwantar dakaiba.”
Dan mahaifinta yasan kasar kano kuma yasan irin mutanen dake cikinta. ”
Amma ace wanda yake mulkarsune ya kwantar dakai wajn neman auren ‘yarsa.”
Haka akaturo magabata aka gama komai. ” kilishi
Bakaramin tashin hankali ta shigaba da wannan zance.”
Sanin bawani sonta yakeyiba yanzu kuma yasamu wacce yakeso, kuma balarabia. ”
Da zigin mahaifiyarta suka fara shiga bokaye da sunan malamai amma bbu abinda yafasu dan aurekam sanda akayishi.” sai bayan aurnne yasan cewa wannan shagon daya ganta ashe shagon mahaifinta ne, sosai yake iya gwargwado na nuna adalci atsakaninsu. ”
Amma duk da haka kilishi tananan da kishinta, saidai kokad’an batada bakar zuciyarda zata cutarda raheema (ummii).”
Hakadai zamnnasu yake ita bawani shiri sukayi ba amma kuma ba fad’a ba. ”
Bayan auren da wata biyu da koma Dubai dan k’arasa karatun ta.”
Tafiyanta ta da d’an wata hudu kilishi ta haihu ta haifi mace, yamayar mata da sunan kanwarsa khadija. ”
Ummii tazo suna, gama ta arkizi ta had’o mata dan harda zinare.”
Lokacin ita kuma cikinta na kinamin wata biyar. ”
Ganin cikin baid’agawa kilishi hankali ba dan tasan ko yanzu itace da gida.”
Bayan wata hud’u tagama karatunta. ”
Ak’asar haihuwa ta sameta.” anan ta haiho danta namiji kyakkyawan gaske. ”
Kafin suna suka dawo Nigeria.”
Asuna yaro yaci sunan kakansa Abudullahi. ”
Iya buduri anyishi,
Wanda kowa mamakin hakan yakeyi dan ko sunan isma’il yareema, ba’ayi buduri haka ba.”
Aikuwa yaron yashiga ran fulani, mahaifiyar mai martaba. ”
Kullum yaron yana wajanta, hakan kuwa bakaramin k’ona ran kilishi yayiba,”
Wajen mahaifiyar ta taje ta shaida mata da kuka. ”
Ran mahaifiyar ta yabaci tana ganii ga wanda yafito d’an dangi nan sai wani bare zataso.”
Bayadda basuyi naraba shi da itaba amma abu yaci tura haka dai aikinsu baiyiba su kuma basu hakura ba. ”
Yafara girman a kullum kyawunsa ne yake dad’a fitowa.”
Yanad’an shekara shida aka daukeshi zuwa makaranta a russia. ”
Fulani kuka tayi tayi akan baza’a kaimata jika kasar arna ba amma haka bayadda ta’iya, haka Ummii ba bawai taso bane.”
Kowani bawan Allah yaji wannan abu saiya tsaya jimami ace yaro tunyana karami da’a daukeshi zuwa wata makaranta. ”
Haka dai aka tafi dashi bawai danran kowa yasoba, abinda yad’an ragewa Ummii zafi dalilin lokacin ta haifi afeeya.”

 

 

 

Sai bayan shekara shidda, kafin yake dawowa hutu, sai dai iyayenshi suna zuwa wajenshi, makarntar ta sojoji ne tun suna k’anana ake kaisu, yakanyi wuya asamu wanda ya fara tundaka farko har ya gama.” wasu idan suntafi hutu basa ta6a dawowa, wasu kuma yawanci da girman su suke zuwa ba rainon makarntar bane,
duk hutunda yazo yakanyi 5-6 month kafin yakoma. ”
Shekara shidan farko yadawo yasamu labarin mutuwar yayansa, yareema isma’ill sakamakon hatsarin mota.”
Sosai mutuwar tashigi ‘yan gidan dan yafara girman yakai kusan 16yrs lokacin. ”
Shima mutuwar ta shigeshi sosai dan Kowani zuwanda za’ ayi masa tareda yayansa ake zuwa.”
Daga nan kuma duk wani soyayya ta tattaro tadawo kansa. ”

 

 

Shekaransa 18 a makarantar alokacin yagama inda duk yanda sadauki da jarumta takai to yakai, masu karatu basaina tsaya yimuku vayani ba kunsan yanda sojojin rusia suke duk duniya bbu sojojin da suka kaisu horuwa, kuyi imagine wanda yayi shekara 18 yana horuwa akasar.”
Duk ciki su uku ne suka fita shine wanda yazo nafaarko. ”
Dan tunda suke ba’atabayin jarumin d’alibi kamarsa ba.”
Hakanne da suka gani sun tabbatar idan yatafi k’asarsa wannan horo dasuka masa yatashi abanza. ”
Ganin Hakanne yasa suka ce sudasu rikeshi.”
Aranda akazo passing out dinsu ne, alokacin duk wani family dinsa sun hallara. ”
Mamaki ne yacika mutanen gani duk bak’ak’en fata ne danginsa.”
Sunga su kansu ma yafisu kyau. ”
Duk wanda akagani awajen taron har inde daga family din MG yafito to karramawarsu dabannee.”
Kowa nema yake ya gaisa dashi ko family dinshi,
Duk wani kyauta shiyasamesu,
Inda kasashe da dama suka bid’ar yamusu aiki. ”
Ganin Kowani kasa na bukatarsa yasa, kowacce tasa hanu aka bugamar starm na sojan k’asa da k’asa.”
Haka taron ya watse kowa na farinciki,
Barin family na MG dasukejin kansu asama. ”
Tunda intisar tad’aura ido akansa, taji tanasonsa, dafarko yad’an fara kulata, amma tunda yayi wata yafiya yadawo yabirkicewa kowa dan ko kallon arziki bata samu.”

Sadam ne yad’an nisa sannan yace ”
Ayanzu haka labarin da nake baku, yaran mahaifinsu shida, khadija, abudullahi (MG), afeeya, affan halima da labba.

Sannan ya nisa yace wannane takaiceccen tarihinsa.”
Daya daga cikinsu ne yace, amma duk wani pics da labarin bbu hoton wannan yarinyar aciki. ”
Me hakan yake nufi kenan?”
Ita wacece idan ba daga cikin family dinsa takeba? ”
Dayanne yace tabbas tana da mahimmanci awajensa, dan wayanna sojojinsa ne.”
Sadam ne ya nisa sannan yace, tabbas dan alabarinda muka samo mungano tun shekarar daya dawo biyu daga cikin sojojin sa are missing kuma haryau bbu wanda yasan yanda suke. ”

Nisawa yayi sannan yace toh kanemo mana ita wannan yarinyar wacece?”.

 

To be continued

Ur’s
_Z33yyb3rwr3r_

[12/2, 9:28 AM] Anty Jamila D Ili: *BIBIYATA AKEYI*
_
_Bismillahirahmanirrahim_

_
Writting by

© _zaynab_ _bawa_
( _z33yyb3rw3r_ )

My first novel

Leave a Comment





No one has commented yet. Be the first!
Leave a Reply