Hausa Novels Sakon So Hausa Novel

Sakon So 4


Sakon So 4
Viral

EPISODE 4️⃣

 

Sister Nace ba 100k din nan dakike ajiya, na siyan GOLD Dinnan…? Yawwa Ashe Kingane, nacikin akwatin NAN…… yawwaaaa Su😂

Nasamo miki wani hanya da zaki anfana dashi, kiyi kudi, kiyawata kasashe daban ban afadin duniyan nan, ke infact harma kisiyi gwala-gwalai dashi harsai kingaji… kinsan bana kawoo muku abun banxa. Sai wanda zaki anfana saboda inasan fans dina suma su dan-dana soft life dinnan fa😂😘

Haba Zainab kinkwantar da hankalinki, xan fada mana😂 saurin mea kikeyi🌝

To ita wannan sannan danajea ngama bincike akai sunan shi AFFILIATE MARKETING…. Dayawanku kunsan Affiliate marketing, musammam Art student..

But duk dahaka Bari inyi masu ooni bayani🌝

Affiliate Marketing sanaa ce da mutun zai siyarda kayan wani sannan abiyashi ribar tasa (hold on nasan xakice ai wannan kaman siyarda abayane abiyaka, nidai gaskia bazn iyaba😐) ki kwantar da hankalinki oo, ya kina mun haka🥹 ba kalan wannan sanaar bace fa, wannan yamafi shi dadi sannan ga sauki. Shide wannan Digital Products e xaki na siyarwa instead of physical, wannan yana nufin bama sai anga fuskarki ba kokuma kinfita daga dakin ki, akan gadanki ma sai kiyi abunki Kuma abiyaki, Yaya yakea.?? Am getting to it😂 wannan platform ne daxakiyi registration dasu, kice musu Kinasan kifara siyarmusu da kaya (Digital Product). Nasan anan ma xakice to idan nayi registration dasu taya xan nemo masu siyan kayan.?? Karki damu After Kinyi Registration su xasu nuna miki tayanda xakina samo mutanea harsu dinka siya.

Sannan duka sati ake payout which means Duk iya siyarwan dakikayi ranan Asabar nazuwa zasu bki kudinki. Idan misali kindau kayan 50k kina siyarwa, kinga 25k nakine. Mudauka asatin kinsiyarma da 20 people, kinga Asati kinada 250k🤯 Awata Kuma 1miliyan nea dake🥵 (Not bad ma sanaan daxaki fara da kudi kalilan)

The best part is ribarki idan kinsiyarda guda daya 50% ne maana rabin kudin nakine, sannan akwai inda zaki kai suna sponsoring dinki xuwa kasashen wajea ko kuma suna baki mota iya adadin kayanda kika siyar.

Registration dasu beada wani tsada ..
Anoda best part of it shinea from January to April idan kika siyar da kaya guda 300 zasu baki dan kareriyar waya ( 14 pro max). Idan kikayi 400 sales zasu biya miki kijea Maldives (wata kasace) idan kuma kikayi 600 sales zasu baki Sabuwar Mota Corolla.

Idan kinasan karin bayani ga number nan xan ajea kiyi mata magana. 09133427208 instagram handle @western_hemisphere_ https://bit.ly/3XleqfK

4:30 yabude kofar dakinshi yafito sai zuba uban kamshi yake kana ganin kasan yay wanka dan yasaka wata milk jallabiya gogaggiya mai bala’in laushi yasaka hula fara kwankwasa kaji hadisi, dakin Hamza yafara shiga yatadashi sannan yashiga dakin Abdallah yatadashi yace yay maza yay alwala kafin yagama tada mutanen gidan, fita yayi yawuce dakin Kausar, ahankali yabude kofan da sallama yashiga yakai hannu yakunna wutar dakin tana kwance kan gado ta kudundune cikin bargo tana shargan bacci karasawa gaban gadon yayi ya bubbuga mata katifa ahankali yace “Kausar” bude idanunta tayi cikin muryan bacci tace “Abeeee” hannunshi yamika mata yace “get up and pray” gently tasa hannunta takama nashi hakan yasa yadagota ahankali ta tashi zaune sannan takarasa yaye bargon tamike tsaye tawuce bayi, fita yayi ya tsaya gaban dakin da Maman Aneesarh ke ciki yay knocking yace “Rahama” cikin muryan bacci tace “natashi Ya Imran” knocking dakin da Anty Binta tasauka yayi itama tace ta tashi sannan yasauka kasa direct dakin Hajiya yayi tunda ya hango wuta dakin yasan ta tashi amman dudda haka sallama yayi yabude yashiga zaune take kan lallausan dadduma da charbi ahannunta hannu tadagamai alamun addu’a take mikewa yayi yafita daidai Hamza da Abdallah sun sauko kasa suka wuce masallaci.

Hamza da Abdallah sun rigashi dawowa daga masallaci danshi dama yana tsayawa yay azkar sannan yagaisa da mutan unguwa idan ana bukatan wani abu a masallacin ya saya, wajajen 7 yashigo gidan da sallaman shi chan ciki, gabaki dayan yaran gidan na falo dukansu an musu wanka looking neat dukansu sun saka kayan makaranta little Aneesarh ne kawai bata fara school ba, kuma duka yaran dsame school suke duk sun zauna suna jiran breakfsat dan iyayensu na kitchen, zama yayi akan kujera one sitter wanda wajen kusan shine wajen zamanshi na ka’ida duka yaran tahowa wajenshi sukayi sannan suka duka atare sukace “Assalamu Alaykum Abee good morning” dan murmushi ya sakan musu yace “wa’alaykumus salam children morning” daidai nan Abdallah shima yashiga saukowa kana ganinshi kasan yay wanka yasa kananun kaya masu kyau da sneakers akafanshi dawata jaka na LV abayanshi sai key mota kaganshi sak ubanshi yana zuwa gaban Abee yace “good morning Abee” “morning Abdallah what time kakeda lectures yau” yana gyara agogon hannunshi yace “Abee by 8 ne yanzu 7 harda minti goma bari nai sauri idan lecturer ya shiga baya kara bari wani yashiga” yay maganan yana mikewa zai wuce Abee yace “go and have breakfast kafin kafita” strictly Abee yay maganan daidai nan Hajiya tafito tace “Alhamdulillah ai yau uban naka nagida naga ta yanda zaka tafi makaranta bakai kari ba yaro kwata kwata bayason cin abinci” turo baki yama Hajiya yajuya yawuce dinning danyi kari Abee yadauke idanunshi daga kanshi yajuya yakalli Hajiya data zauna kan 2 sitter dake facing nashi ahankali yace “ina kwana Hajiya” “mun tashi lpy Imran” ahankali yace “Alhamdulillah Hajiya” yadanyi shiru sai chan yakalleta yace “me kuke bukata agidan”? Anatse Hajiya tace “fruits ne kawai babu amman akwai kayan abinci da komi lastweek ai kasa Hamza yayo chefene” gyadamata kai yayi yace “magungunan kifa”? Tana kallonshi tace “basu kareba har yanzu” daidai nan su Anty Binta suka fito daga kitchen zasu fara jera abinci a dinning Hajiya tace “ku kawo nan muci anan dan Allah ni wlh bason cin abinci wajen nan nakeba” kawo abincin sukayi duk suka gaida yayan nasu Sajida yafara kallo batare daya amsa gaisuwanta ba yace “when are you going back to your husband house”? Murmushi tayi tace “Yaya dazaran yadawo daga lagos zaizo yadaukeni next week yace zaizo ni wlh banma gaj…..” mugun kallon daya mata yasa tahadiye maganan yakalli Zainab kafinma yayi magana da sauri tace “Yaya Imran ni sai ranan Friday kaga yau monday” dan dariya Hajiya tayi tace “yara duk sun zo sun taremini gida sun hanani sakat” turo baki Zainab tayi tace “bamason rabuwa dake Hajiya” dasauri Hajiya tace “aure kam yagaji haka ingayamuku” daidai nan Anty Binta takalli Abee tace “mezan zuba maka akwai waina da pepper soup na cowtail, saikuma chips da egg, akwai kuma dumamen tuwo da kuka sai shayi da kunun gyada” ahankali yace “I want masa da shayi” murmushi tayi tashiga zubamai daidai nan Hamza ya sauko ya shirya cikin suit yayi kyau Hajiya dake kallonshi tace “kai lpy kaci suit yau”? Murmushi yayi yakalli Ya Imran da ake bama abinci yace “yau zamuyi baki a office za’a kawo wasu yan makaranta excursion suga company namu idan Ya Imran yayi welcoming nasu nine let’s just say tourist dinsu to kinga I need to look good” tabe baki Maman Aneesarh tayi yadaga mata gira daya Hajiya ta kalli Abee daya fara kurban shayi ahankali anatse tace “zakuyi baki shine kai me kampani gabaki daya ko shiryawa bakayiba” ahankali yazare kofin shayin daga bakinshi yace “idan nagama zan shirya” zama Hamza yayi yakarbi abincin da Anty Binta ke bashi yace “wlh yaran nan naku suyi sauri inba hakaba babu makarantan dazan kaisu saidai ku ku kaisu” Hajiya ta dubi Anty Binta dake bama yara abincin tace “wai ina jikata Kausara ne jama’an gida”? Dan dariya daga Binta, Sajida, Zainab da Maman Aneesarh sukayi, Maman Aneesarh tace “Hajiya kin manta shiryawan Kausar ne” Zainab tace “manyan yammata yan 100 level JJC saida gayu” daidai nan Abdallah yatashi daga dinning yace “nina tafi” atare kowa na dakin yace “Allah kiyaye hanya, Allah bada sa’a Doctor” karasowa wajen Abee dahar lokacin shayi yakesha baima taba wainar da aka zubamai ba yace “Abee natafi” hannu Abee yasa a aljihu 10k yaciro yabashi dasauri yakarba yana murmushi yace “thank you Abee” ahankali yace “drive safe” murmushi yayi yace “I promise Abee” yajuya dasauri yawuce daidai nan Kausar ta sauko tana sanye da doguwan rigan atampa mai kyau tasaka bakin safa akafanta da flat shoe sannan tarike milk hijabinta ahannu, da dankwalinta a hannu, da jaka da ribbon a hannu tana shigowa ajiyesu tayi akan kujera tazo wajen Abee da sauri tabashi ribbon din tace “Abee kamamini gashin” baki Hajiya tasake tace “yanzu kiwuce duka matan dake dakin nan kitafi wajen ubanki yamiki parking gashi dakecin abinci” turo baki tayi tawuce tabama Zainab tace “samin Anty” murmushi tayi takama gashin da baida wani tsawo tace “kawo kallabin na daura miki shima kawowa tayi tadaura mata sannan tazauna tana breakfsat dasauri sauri hada ido tayi da Abee dake kallonta, kallon daya mata kadai yasa ta faracin abincin ahankali anatse dan yahanata cin abinci da sauri adolenta ta natsu ta cinye tass sannan ta tashi tasaka hijabinta itada sauran yaran sukabi Ya Hamza dazai kaisu sukabar gidan.

 

2 slice na waina yaci acikin hudun da aka sakamishi sannan yatashi yawuce sama dan shiryawa, tsaf ya shirya cikin black suit dayasaka wata farar Riga aciki mai shegen kyau, baisa boturin jacket na suit dinba hakan yasa kana iya ganin farin, yasa black Wandon suit din daya tsayamai a idon sahu as usual yanda tsayin wandunanshi suke, covershoe yasaka na gucci dake wani shining, wannan karan babu any hula akanshi hakan yasa gashin kanshi yay wani kalan kyau ya kwanta lub sai kyalli suke, ahankali yake saukowa rikeda wata jakan laptop a hannunshi daga Hajiya har duka matan ta duk suna falo da Matan Ibro itama yanzun nan tashigo tanacin ragowan waina dan tsohon ciki ne da ita bata iyacin abincin data dafa, ganin Abee yasa akunyace ta sauke kanta dan kowa nauyin Abee yakeji cikeda kunya tace “ina kwana Abee” kallo daya yamata yadauke kai yace “Alhamdulillah” yakalli Hajiya yace “natafi Hajiya” dan murmushi tasakin mai tace “ubangiji Allah yabada sa’a yakara daukaka” ahankali yace “Ameen” su Anty Binta atare sukace “Allah bada sa’a Yaya” bai amsasu ba yafice suna sonshi bana wasaba Ya Imran shine komi nasu, ci sha sutura, duka kanninshi dukansu duk wata kowacce yana bata kyautan kudi hatta matan Ibro, banda Ibro da Hamza da suma tunda sun gama makaranta duka yasasu a company shi duk suna aiki awajen, school fee na marayun yaran Maman Aneesa na kanshi magani komi, sai su Abdallah da Kausar dake university Kausar this year tafara tana 100level tana karantan Mass com, shikuma Abdallah na 300 level medicine, Abdallah nada bala’in kokari da kwazo ga natsuwa da tausayi da kirki saisa Abee yabashi motan kanshi dudda he’s 22yrs dan yawanci early morning lectures yake kuma bayida gara gara, itama Kausar tana kokari ba laifi amman ba kaman Abdallah ba randa sukeda lectures lokaci daya da Abdallah shi yake wucewa da ita idan kuma ya bambamta Hamza ke kaita.

Leave a Comment





No one has commented yet. Be the first!
Leave a Reply